Tun daga ranar 1 ga watan Mayu, kasar Sin ta fara aiwatar da matakin soke haraji baki daya kan hajojin kasashen Afirka 53 da ke da huldar diplomasiyya da ita.
Game da batun, shugaban hukumar kungiyar AU Mahamoud Ali Youssouf ya yaba wa matakin, yana cewa ya dace da nahiyar Afirka a wannan lokacin da kasashenta suke fuskantar kalubale sakamakon yake-yaken da suke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya.
Mahamoud Ali Youssouf ya bayyana hakan ne yayin zantarwa da wakilin babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG, inda ya kara da cewa, matakin Sin ya nuna zumunci mai zurfi dake tsakaninta da kasashen Afirka, wanda ya kawo kuzari ga jama’ar kasashen Afirka.
Kana ya yi kira ga kasa da kasa da su maida hankali ga ra’ayoyin kasashen Afirka, da kafa ka’idojin yin ciniki a tsakanin bangarori daban daban masu adalci.
Hakazalika kuma, ya yaba wa kasar Sin bisa yadda ta amsa kiran kasashen Afirka, da hada hannu da kasashen wajen samun ci gaba tare ta hanyar taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka FOCAC da sauransu. (Zainab Zhang)















Discussion about this post