Cancantar zuwa gasar kofin Afrika 2027 ta fara bayyana, inda tawagar Nijeriya za ta san abokan karawarta a matakin neman tikitin shiga gasar a ranar 19 ga watan Mayu, lokacin da za a gudanar da zaɓen rukuni.
Jimillar ƙasashe 48 ne za su fafata a wasannin neman tikitin, ciki har da ƙasashen da za su karɓi baƙuncin gasar wato Kenya, da Tanzania da Uganda, waɗanda duk za su shiga fafatawar duk da kasancewarsu masu masaukin baƙi.
Za a gudanar da wasannin ne cikin gajeren lokaci a cikin lokutan FIFA uku na bana, wato Satumba, da Oktoba da Nuwamba, wanda hakan zai sa fafatawar ta kasance mai zafi da sauri wajen neman gurbin shiga babbar gasar nahiyar.
A tsarin da aka amince da shi, za a raba ƙasashe 48 zuwa rukuni 12, kowanne rukuni na ɗauke da ƙasashe huɗu. Ƙasashe biyu na farko daga kowanne rukuni ne kawai za su samu tikitin shiga gasar, lamarin da ke ƙara muhimmanci ga kowanne wasa.
Super Eagles na shiga wannan fafatawa da ƙwarin gwuiwa bayan da ta samu matsayi na uku a gasar AFCON 2025 da aka gudanar a Morocco. Hukumar Confederation of African Football ta tabbatar da cewa za a fara gasar AFCON 2027 a ranar 19 ga Yuni, 2027, sannan za a kammala a ranar 17 ga Yuli, 2027, a karon farko da ƙasashe uku za su karɓi baƙuncin gasar tare.















Discussion about this post