A wajen taron tattaunawa kan aikin tsaro na Shangri-La karon 23 dake gudana a kasar Singapore, shugaban tawagar masanan rundunar kasar Sin, Meng Xiangqing ya yi wani jawabi mai taken “A sa kaimi ga yunkurin tabbatar da kwanciyar hankali a duniya”.
A cewar Mista Meng, tsarin kare tsaro a duniya na fuskantar dimbin kalubaloli, lamarin da ya sanya kasar Sin gabatar da shawarwari na karfafa tsaro a duniya, da kula da al’amuran kasa da kasa yadda ya kamata, da tsayawa kan ra’ayin tabbatar da tsaro irin na bai daya, da hadin gwiwa, wanda kuma zai dore.
Ban da haka, kasar Sin ta bukaci kasashe daban daban, da su rungumi ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da na kulawa da al’amuran duniya bisa doka, gami da kokarin kafa wani tsarin tabbatar da tsaro mai adalci a duniya.
Dangane da aikin kiyaye tsarin kasa da kasa da aka tabbatar da shi bayan da aka kawo karshen babban yakin duniya na biyu, shugaban na tawagar masanan tawagar kasar Sin ya ce, ya kamata a magance farfado da ra’ayin fin karfin soja a kasar Japan. A cewarsa, kasar Japan ba ta taba kawar da mummunan ra’ayin daga tushe ba, saboda haka yana matukar shakku kan dacewar yunkurin baiwa kasar Japan damar hadin gwiwa da sauran kasashe ta fuskar aikin tsaro, da samun amincewa daga al’ummun kasa da kasa, musamman ma na kasashen Asiya da kasar Japan ta taba kaiwa hari.
Kana a yayin da yake tsokaci kan batun nukiliya, Mista Meng ya ce, kasar Sin ta bayyana ra’ayinta dangane da wannan batu sarai, kuma matsayinta bai taba sauyawa ba, wato tana tsayawa kan manufar raya fasahar nukiliya ta hanyar lumana, inda take mallakar wasu makaman nukiliya don kare kanta kadai, kuma ta yi alkawarin cewa ba za ta zama mai fara amfani da makaman ba.
Ban da haka, kasar tana son ganin an kawar da makaman nukiliya a dukkan kasashe masu makaman.Haka zalika, a gefen taron tattauna batun tsaro na Shangri-La dake gudana a wannan karo, Mista Meng ya zanta da wakilin kafar yada labarai ta CMG, inda ya yi tsokaci kan huldar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka.
Ya ce, shugabannin kasashen 2 sun riga sun cimma matsaya daya, ta raya “dangantaka mai karko da yakini, wadda ta shafi manyan tsare-tsare” tsakanin kasashensu, abun da ya tabbatar da alkibla ga aikin raya hulda a tsakanin kasashen 2 da kuma sojojinsu. Saboda haka, ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi kokarin hadin gwiwa da juna, don kiyaye tsaro da kwanciyar hankali a yankunan da suke ciki, har ma a dukkanin fadin duniya baki daya. (Bello Wang)















Discussion about this post