ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: A Sa Kaimi Ga Yunkurin Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
A man stands near the entrance of the Shangri-La Hotel, the venue for the International Institute for Strategic Studies (IISS) Shangri-La Dialogue, Asia's annual defense and security forum, in Singapore, Thursday, May 28, 2026. (AP Photo/Achmad Ibrahim)

A man stands near the entrance of the Shangri-La Hotel, the venue for the International Institute for Strategic Studies (IISS) Shangri-La Dialogue, Asia's annual defense and security forum, in Singapore, Thursday, May 28, 2026. (AP Photo/Achmad Ibrahim)

A wajen taron tattaunawa kan aikin tsaro na Shangri-La karon 23 dake gudana a kasar Singapore, shugaban tawagar masanan rundunar kasar Sin, Meng Xiangqing ya yi wani jawabi mai taken “A sa kaimi ga yunkurin tabbatar da kwanciyar hankali a duniya”.

A cewar Mista Meng, tsarin kare tsaro a duniya na fuskantar dimbin kalubaloli, lamarin da ya sanya kasar Sin gabatar da shawarwari na karfafa tsaro a duniya, da kula da al’amuran kasa da kasa yadda ya kamata, da tsayawa kan ra’ayin tabbatar da tsaro irin na bai daya, da hadin gwiwa, wanda kuma zai dore.

Ban da haka, kasar Sin ta bukaci kasashe daban daban, da su rungumi ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da na kulawa da al’amuran duniya bisa doka, gami da kokarin kafa wani tsarin tabbatar da tsaro mai adalci a duniya.

ADVERTISEMENT

Dangane da aikin kiyaye tsarin kasa da kasa da aka tabbatar da shi bayan da aka kawo karshen babban yakin duniya na biyu, shugaban na tawagar masanan tawagar kasar Sin ya ce, ya kamata a magance farfado da ra’ayin fin karfin soja a kasar Japan. A cewarsa, kasar Japan ba ta taba kawar da mummunan ra’ayin daga tushe ba, saboda haka yana matukar shakku kan dacewar yunkurin baiwa kasar Japan damar hadin gwiwa da sauran kasashe ta fuskar aikin tsaro, da samun amincewa daga al’ummun kasa da kasa, musamman ma na kasashen Asiya da kasar Japan ta taba kaiwa hari.

Kana a yayin da yake tsokaci kan batun nukiliya, Mista Meng ya ce, kasar Sin ta bayyana ra’ayinta dangane da wannan batu sarai, kuma matsayinta bai taba sauyawa ba, wato tana tsayawa kan manufar raya fasahar nukiliya ta hanyar lumana, inda take mallakar wasu makaman nukiliya don kare kanta kadai, kuma ta yi alkawarin cewa ba za ta zama mai fara amfani da makaman ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Ban da haka, kasar tana son ganin an kawar da makaman nukiliya a dukkan kasashe masu makaman.Haka zalika, a gefen taron tattauna batun tsaro na Shangri-La dake gudana a wannan karo, Mista Meng ya zanta da wakilin kafar yada labarai ta CMG, inda ya yi tsokaci kan huldar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka.

Ya ce, shugabannin kasashen 2 sun riga sun cimma matsaya daya, ta raya “dangantaka mai karko da yakini, wadda ta shafi manyan tsare-tsare” tsakanin kasashensu, abun da ya tabbatar da alkibla ga aikin raya hulda a tsakanin kasashen 2 da kuma sojojinsu. Saboda haka, ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi kokarin hadin gwiwa da juna, don kiyaye tsaro da kwanciyar hankali a yankunan da suke ciki, har ma a dukkanin fadin duniya baki daya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Next Post
Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

LABARAI MASU NASABA

Sin

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Sin

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.