ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: A Sa Kaimi Ga Yunkurin Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 weeks ago
A man stands near the entrance of the Shangri-La Hotel, the venue for the International Institute for Strategic Studies (IISS) Shangri-La Dialogue, Asia's annual defense and security forum, in Singapore, Thursday, May 28, 2026. (AP Photo/Achmad Ibrahim)

A man stands near the entrance of the Shangri-La Hotel, the venue for the International Institute for Strategic Studies (IISS) Shangri-La Dialogue, Asia's annual defense and security forum, in Singapore, Thursday, May 28, 2026. (AP Photo/Achmad Ibrahim)

A wajen taron tattaunawa kan aikin tsaro na Shangri-La karon 23 dake gudana a kasar Singapore, shugaban tawagar masanan rundunar kasar Sin, Meng Xiangqing ya yi wani jawabi mai taken “A sa kaimi ga yunkurin tabbatar da kwanciyar hankali a duniya”.

A cewar Mista Meng, tsarin kare tsaro a duniya na fuskantar dimbin kalubaloli, lamarin da ya sanya kasar Sin gabatar da shawarwari na karfafa tsaro a duniya, da kula da al’amuran kasa da kasa yadda ya kamata, da tsayawa kan ra’ayin tabbatar da tsaro irin na bai daya, da hadin gwiwa, wanda kuma zai dore.

Ban da haka, kasar Sin ta bukaci kasashe daban daban, da su rungumi ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da na kulawa da al’amuran duniya bisa doka, gami da kokarin kafa wani tsarin tabbatar da tsaro mai adalci a duniya.

ADVERTISEMENT

Dangane da aikin kiyaye tsarin kasa da kasa da aka tabbatar da shi bayan da aka kawo karshen babban yakin duniya na biyu, shugaban na tawagar masanan tawagar kasar Sin ya ce, ya kamata a magance farfado da ra’ayin fin karfin soja a kasar Japan. A cewarsa, kasar Japan ba ta taba kawar da mummunan ra’ayin daga tushe ba, saboda haka yana matukar shakku kan dacewar yunkurin baiwa kasar Japan damar hadin gwiwa da sauran kasashe ta fuskar aikin tsaro, da samun amincewa daga al’ummun kasa da kasa, musamman ma na kasashen Asiya da kasar Japan ta taba kaiwa hari.

Kana a yayin da yake tsokaci kan batun nukiliya, Mista Meng ya ce, kasar Sin ta bayyana ra’ayinta dangane da wannan batu sarai, kuma matsayinta bai taba sauyawa ba, wato tana tsayawa kan manufar raya fasahar nukiliya ta hanyar lumana, inda take mallakar wasu makaman nukiliya don kare kanta kadai, kuma ta yi alkawarin cewa ba za ta zama mai fara amfani da makaman ba.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Ban da haka, kasar tana son ganin an kawar da makaman nukiliya a dukkan kasashe masu makaman.Haka zalika, a gefen taron tattauna batun tsaro na Shangri-La dake gudana a wannan karo, Mista Meng ya zanta da wakilin kafar yada labarai ta CMG, inda ya yi tsokaci kan huldar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka.

Ya ce, shugabannin kasashen 2 sun riga sun cimma matsaya daya, ta raya “dangantaka mai karko da yakini, wadda ta shafi manyan tsare-tsare” tsakanin kasashensu, abun da ya tabbatar da alkibla ga aikin raya hulda a tsakanin kasashen 2 da kuma sojojinsu. Saboda haka, ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi kokarin hadin gwiwa da juna, don kiyaye tsaro da kwanciyar hankali a yankunan da suke ciki, har ma a dukkanin fadin duniya baki daya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.