ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: A Sa Kaimi Ga Yunkurin Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago
A man stands near the entrance of the Shangri-La Hotel, the venue for the International Institute for Strategic Studies (IISS) Shangri-La Dialogue, Asia's annual defense and security forum, in Singapore, Thursday, May 28, 2026. (AP Photo/Achmad Ibrahim)

A man stands near the entrance of the Shangri-La Hotel, the venue for the International Institute for Strategic Studies (IISS) Shangri-La Dialogue, Asia's annual defense and security forum, in Singapore, Thursday, May 28, 2026. (AP Photo/Achmad Ibrahim)

A wajen taron tattaunawa kan aikin tsaro na Shangri-La karon 23 dake gudana a kasar Singapore, shugaban tawagar masanan rundunar kasar Sin, Meng Xiangqing ya yi wani jawabi mai taken “A sa kaimi ga yunkurin tabbatar da kwanciyar hankali a duniya”.

A cewar Mista Meng, tsarin kare tsaro a duniya na fuskantar dimbin kalubaloli, lamarin da ya sanya kasar Sin gabatar da shawarwari na karfafa tsaro a duniya, da kula da al’amuran kasa da kasa yadda ya kamata, da tsayawa kan ra’ayin tabbatar da tsaro irin na bai daya, da hadin gwiwa, wanda kuma zai dore.

Ban da haka, kasar Sin ta bukaci kasashe daban daban, da su rungumi ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da na kulawa da al’amuran duniya bisa doka, gami da kokarin kafa wani tsarin tabbatar da tsaro mai adalci a duniya.

ADVERTISEMENT

Dangane da aikin kiyaye tsarin kasa da kasa da aka tabbatar da shi bayan da aka kawo karshen babban yakin duniya na biyu, shugaban na tawagar masanan tawagar kasar Sin ya ce, ya kamata a magance farfado da ra’ayin fin karfin soja a kasar Japan. A cewarsa, kasar Japan ba ta taba kawar da mummunan ra’ayin daga tushe ba, saboda haka yana matukar shakku kan dacewar yunkurin baiwa kasar Japan damar hadin gwiwa da sauran kasashe ta fuskar aikin tsaro, da samun amincewa daga al’ummun kasa da kasa, musamman ma na kasashen Asiya da kasar Japan ta taba kaiwa hari.

Kana a yayin da yake tsokaci kan batun nukiliya, Mista Meng ya ce, kasar Sin ta bayyana ra’ayinta dangane da wannan batu sarai, kuma matsayinta bai taba sauyawa ba, wato tana tsayawa kan manufar raya fasahar nukiliya ta hanyar lumana, inda take mallakar wasu makaman nukiliya don kare kanta kadai, kuma ta yi alkawarin cewa ba za ta zama mai fara amfani da makaman ba.

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Ban da haka, kasar tana son ganin an kawar da makaman nukiliya a dukkan kasashe masu makaman.Haka zalika, a gefen taron tattauna batun tsaro na Shangri-La dake gudana a wannan karo, Mista Meng ya zanta da wakilin kafar yada labarai ta CMG, inda ya yi tsokaci kan huldar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka.

Ya ce, shugabannin kasashen 2 sun riga sun cimma matsaya daya, ta raya “dangantaka mai karko da yakini, wadda ta shafi manyan tsare-tsare” tsakanin kasashensu, abun da ya tabbatar da alkibla ga aikin raya hulda a tsakanin kasashen 2 da kuma sojojinsu. Saboda haka, ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi kokarin hadin gwiwa da juna, don kiyaye tsaro da kwanciyar hankali a yankunan da suke ciki, har ma a dukkanin fadin duniya baki daya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni
  • Sulaiman
    Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya
  • Sulaiman
    Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
  • Sulaiman
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

MASU ALAKA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
Daga Birnin Sin

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
Daga Birnin Sin

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
Next Post
Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

July 5, 2026
Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

July 5, 2026
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

July 5, 2026
Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

July 5, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 5, 2026
Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.