ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

by Sani Anwar
1 month ago

Dakarun Operation Haɗin Kai (OPHK), sun ceto wasu da aka yi garkuwa da su, su kimanin 92 tare da daƙile wani harin bam da aka kai a wani samame da suka yi cikin gaggawa a hanyar Buratai zuwa Kamuya a Ƙaramar Hukumar Biu ta Jihar Borno.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Lt.-Col. Sani Uba, ya fitar ranar Lahadin da ta gabata.

Uba ya ce, sojojin na bataliya ta musamman ta 135 da aka tura Dutse Kura ne suka kai farmakin, biyo bayan gano ƴan ta’addan Boko Haram/ISWAP da suka yi awon gaba da mutane da motocin da suka yi garkuwa da su cikin daji a cikin kimanin awa 1122.

ADVERTISEMENT

Ya ce, nan take sojojin suka tura dakarun gaggawa tare da haɗin gwiwar runduna ta 27 ta ‘Task Force Brigade Garrison’, domin daƙile ƴan ta’addan.

Ya ce, wannan haɗaka da aka yi, ta tilasta wa maharan barin mutanen da suka yi garkuwa da su, suka gudu cikin ruɗani zuwa yankin Mangari zuwa Dora.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

A cewarsa, an yi nasarar ceto jimillar mutane 92 da aka yi garkuwa da su, da suka haɗa da maza 52, mata 33 da yara bakwai da kuma motoci takwas.

“Ƴan ta’addan da suka tsere, a ƙoƙarinsu na jinkirta bin su, an bayar da rahoton dasa bama-bamai guda uku (IEDs) a kan hanyar Bula Zarma zuwa Mangari.”

“Ƙungiyoyin Kashe Bama-Bamai (EOD), sun amsa cikin gaggawa tare da samun nasarar kawar da duk na’urori uku, tare da share hanya don ci gaba da gudanar da ayyukansu.

“Sojoji sun yi tazarar kilomita biyar, bayan babban yankin Mangari, yayin da binciken da aka gudanar ya nuna cewa; ƴan ta’addan sun watse cikin firgici da ruɗani, inda suka yi watsi da manufar tasu,” in ji shi.

Uba ya tabbatar da cewa, ba a samu asarar ma’aikata ko kayan aiki ba, a yayin farmakin.

Ya ce, an bai wa fararen hular da aka ceto tallafin jin ƙai cikin gaggawa, sannan aka raka su Damaturu, domin ci gaba da tafiya zuwa inda suke.

A cewarsa, babban hafsan sojin ya yaba wa sojojin, bisa ƙwarewa da kuma gaggawar mayar da martani, yana mai bayyana aikin a matsayin wani nuni na ingantacciyar damar sa ido, isar da aiki da kuma shirye-shiryen yaƙi.

Haka zalika, ya nanata ƙudurin hukumar na ci gaba da matsin lamba kan ƴan ta’addan da kuma tabbatar da tsaron fararen hula a faɗin yankin Arewa-maso-gabas. 

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Next Post
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Tallafin Magunguna Ga Hukumar Kiwon Lafiya Ta Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Tallafin Magunguna Ga Hukumar Kiwon Lafiya Ta Saliyo

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.