ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

by Sani Anwar
3 weeks ago

Dakarun Operation Haɗin Kai (OPHK), sun ceto wasu da aka yi garkuwa da su, su kimanin 92 tare da daƙile wani harin bam da aka kai a wani samame da suka yi cikin gaggawa a hanyar Buratai zuwa Kamuya a Ƙaramar Hukumar Biu ta Jihar Borno.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Lt.-Col. Sani Uba, ya fitar ranar Lahadin da ta gabata.

Uba ya ce, sojojin na bataliya ta musamman ta 135 da aka tura Dutse Kura ne suka kai farmakin, biyo bayan gano ƴan ta’addan Boko Haram/ISWAP da suka yi awon gaba da mutane da motocin da suka yi garkuwa da su cikin daji a cikin kimanin awa 1122.

ADVERTISEMENT

Ya ce, nan take sojojin suka tura dakarun gaggawa tare da haɗin gwiwar runduna ta 27 ta ‘Task Force Brigade Garrison’, domin daƙile ƴan ta’addan.

Ya ce, wannan haɗaka da aka yi, ta tilasta wa maharan barin mutanen da suka yi garkuwa da su, suka gudu cikin ruɗani zuwa yankin Mangari zuwa Dora.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

A cewarsa, an yi nasarar ceto jimillar mutane 92 da aka yi garkuwa da su, da suka haɗa da maza 52, mata 33 da yara bakwai da kuma motoci takwas.

“Ƴan ta’addan da suka tsere, a ƙoƙarinsu na jinkirta bin su, an bayar da rahoton dasa bama-bamai guda uku (IEDs) a kan hanyar Bula Zarma zuwa Mangari.”

“Ƙungiyoyin Kashe Bama-Bamai (EOD), sun amsa cikin gaggawa tare da samun nasarar kawar da duk na’urori uku, tare da share hanya don ci gaba da gudanar da ayyukansu.

“Sojoji sun yi tazarar kilomita biyar, bayan babban yankin Mangari, yayin da binciken da aka gudanar ya nuna cewa; ƴan ta’addan sun watse cikin firgici da ruɗani, inda suka yi watsi da manufar tasu,” in ji shi.

Uba ya tabbatar da cewa, ba a samu asarar ma’aikata ko kayan aiki ba, a yayin farmakin.

Ya ce, an bai wa fararen hular da aka ceto tallafin jin ƙai cikin gaggawa, sannan aka raka su Damaturu, domin ci gaba da tafiya zuwa inda suke.

A cewarsa, babban hafsan sojin ya yaba wa sojojin, bisa ƙwarewa da kuma gaggawar mayar da martani, yana mai bayyana aikin a matsayin wani nuni na ingantacciyar damar sa ido, isar da aiki da kuma shirye-shiryen yaƙi.

Haka zalika, ya nanata ƙudurin hukumar na ci gaba da matsin lamba kan ƴan ta’addan da kuma tabbatar da tsaron fararen hula a faɗin yankin Arewa-maso-gabas. 

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Tallafin Magunguna Ga Hukumar Kiwon Lafiya Ta Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Tallafin Magunguna Ga Hukumar Kiwon Lafiya Ta Saliyo

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.