Dakarun Operation Haɗin Kai (OPHK), sun ceto wasu da aka yi garkuwa da su, su kimanin 92 tare da daƙile wani harin bam da aka kai a wani samame da suka yi cikin gaggawa a hanyar Buratai zuwa Kamuya a Ƙaramar Hukumar Biu ta Jihar Borno.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Lt.-Col. Sani Uba, ya fitar ranar Lahadin da ta gabata.
Uba ya ce, sojojin na bataliya ta musamman ta 135 da aka tura Dutse Kura ne suka kai farmakin, biyo bayan gano ƴan ta’addan Boko Haram/ISWAP da suka yi awon gaba da mutane da motocin da suka yi garkuwa da su cikin daji a cikin kimanin awa 1122.
Ya ce, nan take sojojin suka tura dakarun gaggawa tare da haɗin gwiwar runduna ta 27 ta ‘Task Force Brigade Garrison’, domin daƙile ƴan ta’addan.
Ya ce, wannan haɗaka da aka yi, ta tilasta wa maharan barin mutanen da suka yi garkuwa da su, suka gudu cikin ruɗani zuwa yankin Mangari zuwa Dora.
A cewarsa, an yi nasarar ceto jimillar mutane 92 da aka yi garkuwa da su, da suka haɗa da maza 52, mata 33 da yara bakwai da kuma motoci takwas.
“Ƴan ta’addan da suka tsere, a ƙoƙarinsu na jinkirta bin su, an bayar da rahoton dasa bama-bamai guda uku (IEDs) a kan hanyar Bula Zarma zuwa Mangari.”
“Ƙungiyoyin Kashe Bama-Bamai (EOD), sun amsa cikin gaggawa tare da samun nasarar kawar da duk na’urori uku, tare da share hanya don ci gaba da gudanar da ayyukansu.
“Sojoji sun yi tazarar kilomita biyar, bayan babban yankin Mangari, yayin da binciken da aka gudanar ya nuna cewa; ƴan ta’addan sun watse cikin firgici da ruɗani, inda suka yi watsi da manufar tasu,” in ji shi.
Uba ya tabbatar da cewa, ba a samu asarar ma’aikata ko kayan aiki ba, a yayin farmakin.
Ya ce, an bai wa fararen hular da aka ceto tallafin jin ƙai cikin gaggawa, sannan aka raka su Damaturu, domin ci gaba da tafiya zuwa inda suke.
A cewarsa, babban hafsan sojin ya yaba wa sojojin, bisa ƙwarewa da kuma gaggawar mayar da martani, yana mai bayyana aikin a matsayin wani nuni na ingantacciyar damar sa ido, isar da aiki da kuma shirye-shiryen yaƙi.
Haka zalika, ya nanata ƙudurin hukumar na ci gaba da matsin lamba kan ƴan ta’addan da kuma tabbatar da tsaron fararen hula a faɗin yankin Arewa-maso-gabas.















Discussion about this post