ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

by Sani Anwar
2 months ago

Dakarun Operation Haɗin Kai (OPHK), sun ceto wasu da aka yi garkuwa da su, su kimanin 92 tare da daƙile wani harin bam da aka kai a wani samame da suka yi cikin gaggawa a hanyar Buratai zuwa Kamuya a Ƙaramar Hukumar Biu ta Jihar Borno.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Lt.-Col. Sani Uba, ya fitar ranar Lahadin da ta gabata.

Uba ya ce, sojojin na bataliya ta musamman ta 135 da aka tura Dutse Kura ne suka kai farmakin, biyo bayan gano ƴan ta’addan Boko Haram/ISWAP da suka yi awon gaba da mutane da motocin da suka yi garkuwa da su cikin daji a cikin kimanin awa 1122.

ADVERTISEMENT

Ya ce, nan take sojojin suka tura dakarun gaggawa tare da haɗin gwiwar runduna ta 27 ta ‘Task Force Brigade Garrison’, domin daƙile ƴan ta’addan.

Ya ce, wannan haɗaka da aka yi, ta tilasta wa maharan barin mutanen da suka yi garkuwa da su, suka gudu cikin ruɗani zuwa yankin Mangari zuwa Dora.

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

A cewarsa, an yi nasarar ceto jimillar mutane 92 da aka yi garkuwa da su, da suka haɗa da maza 52, mata 33 da yara bakwai da kuma motoci takwas.

“Ƴan ta’addan da suka tsere, a ƙoƙarinsu na jinkirta bin su, an bayar da rahoton dasa bama-bamai guda uku (IEDs) a kan hanyar Bula Zarma zuwa Mangari.”

“Ƙungiyoyin Kashe Bama-Bamai (EOD), sun amsa cikin gaggawa tare da samun nasarar kawar da duk na’urori uku, tare da share hanya don ci gaba da gudanar da ayyukansu.

“Sojoji sun yi tazarar kilomita biyar, bayan babban yankin Mangari, yayin da binciken da aka gudanar ya nuna cewa; ƴan ta’addan sun watse cikin firgici da ruɗani, inda suka yi watsi da manufar tasu,” in ji shi.

Uba ya tabbatar da cewa, ba a samu asarar ma’aikata ko kayan aiki ba, a yayin farmakin.

Ya ce, an bai wa fararen hular da aka ceto tallafin jin ƙai cikin gaggawa, sannan aka raka su Damaturu, domin ci gaba da tafiya zuwa inda suke.

A cewarsa, babban hafsan sojin ya yaba wa sojojin, bisa ƙwarewa da kuma gaggawar mayar da martani, yana mai bayyana aikin a matsayin wani nuni na ingantacciyar damar sa ido, isar da aiki da kuma shirye-shiryen yaƙi.

Haka zalika, ya nanata ƙudurin hukumar na ci gaba da matsin lamba kan ƴan ta’addan da kuma tabbatar da tsaron fararen hula a faɗin yankin Arewa-maso-gabas. 

Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Zamfara
Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Next Post
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Tallafin Magunguna Ga Hukumar Kiwon Lafiya Ta Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Tallafin Magunguna Ga Hukumar Kiwon Lafiya Ta Saliyo

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.