ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Na Yin Tasiri Mai Yakini A Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Attendees take photographs of themselves in front of a banner at the COP27 climate conference in Sharm El-Sheikh, Egypt, on Sunday, Nov. 6, 2022. Disagreements over who should pay for the harm done by climate-driven extreme weather events will be at the heart of discussions at COP27, the first to be held in Africa since 2016. Photographer: Islam Safwat/Bloomberg

Attendees take photographs of themselves in front of a banner at the COP27 climate conference in Sharm El-Sheikh, Egypt, on Sunday, Nov. 6, 2022. Disagreements over who should pay for the harm done by climate-driven extreme weather events will be at the heart of discussions at COP27, the first to be held in Africa since 2016. Photographer: Islam Safwat/Bloomberg

Wasu abubuwa guda 2 da suka faru a kwanan baya sun nuna hadin gwiwar kut da kut da kasashen Afirka da kasar Sin suke yi a fannin kula da harkokin kasa da kasa.

Daya shi ne yadda Afirka da Sin suka hada kai wajen tabbatar da an zartas da kudurin kafa asusun biyan diya ga kasashe masu tasowa, wadanda suka samu hasara sakamakon bala’un da sauyawar yanayin duniya ke haddasawa, a taron bangarorin da suka sanya hannu kan yarjejeniyar tinkarar sauyawar yanayi ta MDD na COP27, wanda ya kasance wata babbar nasarar da kasashe masu tasowa suka cimma a kokarinsu na muhawara da kasashe masu sukuni.

  • Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Taron MDD Da Sin Kan Huldar Kasa Da Kasa Game Da Binciken Sararin Samaniya

Dayan kuwa shi ne yadda kasar Sin ta nuna goyon baya ga kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU kan batun halartarta kungiyar kasashe masu karfin tattalin arziki ta G20, inda a wajen taron kolin G20 na 17 da ya kammala a kwanakin baya, kasar Sin ta zama mambar kungiyar G20 ta farko da ta nuna goyon baya ga kungiyar AU a fili.

ADVERTISEMENT

Na san wadannan abubuwa za su sanya ku yin tambayar cewa, mene ne ya sa har kullum kasashen Afirka da kasar Sin ke hadin kai da juna, yayin da suke kula da al’amuran kasa da kasa?

A gani na, dalili shi ne, kasar Sin da kasashen Afirka suna da tunani iri daya. Da farko, dukkansu na son tabbatar da yanayi na adalci a duniya. Saboda sun taba shan wahala sakamakon tsare-tsaren duniya da kasashen yammacin duniya ke jagoranta, inda a kan yi musu danniya a fannonin siyasa da tattalin arziki. Wannan niyyar bai daya, ta zama wani tushe mai karfi ga hadin gwiwar Sin da Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Idan mun dauki maganar tinkarar sauyawar yanayin duniya a matsayin misali. Kasashen yamma sun bukaci kasashen Afirka da su dauki nauyin rage fitar da iska mai dumama yanayi iri daya da nasu, ko da yake hakikanin adadin iskar da kasashen Afirka ke fitarwa bai wuce kaso 3 bisa dari na jimillar adadin dukkanin duniya ba. Sai dai a nata bangare, kasar Sin ta jaddada bukatar daukar nauyi mabanbanta tsakanin kasashe masu sukuni da masu tasowa.

Sa’an nan kasar Sin ita ma tana fuskantar matsin lambar da kasashen yamma suke yi mata, inda suke neman soke matsayin kasar na wata kasa mai tasowa, don dora mata matukar nauyi na rage fitar da hayaki da samar da kudi. Duk da haka, kasashen Afirka sun yaba wa kasar Sin kan yadda take kokarin samar da gudunmowa ga aikin raya makamashi masu tsabta a duniya, kana sun bukaci kasashen yamma da su dauki karin nauyi, bisa yadda suka dade suna fitar da dimbin hayaki mai guba cikin shekaru 200 da suka wuce.

Na biyu shi ne, kasashen Afirka da kasar Sin suna dora matukar muhimmanci kan abu daya, wato neman ci gaba. Sabanin yadda wasu kasashen yamma suke dora muhimmanci kan kare ikonsu na yin babakere a duniya, da takara da wasu kasashe, Sin da Afirka na ta kokarin neman hanyar raya kasa. Misali, a taron G20 na wannan karo, kasashen yamma sun fi mai da hankali kan batun dora wa kasar Rasha taken “kasa mai kai hari ga saura”, yayin da a nasu bangare, shugabannin kasashen Afirka da Sin ke nanata kalmomi irinsu “hadin kai”, da “raya kasa”, da “amfanin kowa”, da dai sauransu, a cikin jawaban da suka gabatar.

Ya kamata mu tuna da cewa, yawan al’ummar kasar Sin da ta kasashen Afirka ya kai fiye da kashi 35% na daukacin al’ummar duniya. Duk wadannan mutane masu yawa haka, suna son tabbatar da yanayin adalci a duniya, da kokarin hadin gwiwa don kare moriyar kowa, wannan abun alheri ne ga daukacin ‘yan Adam, wanda ke samar da tasiri mai yakini ga duniyarmu ta wannan zamani. (Bello Wang)

 

 

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Kyautata Musayar Al’Adu Zai Toshe Duk Wata Kafa Ta Baraka Tsakanin Sin Da Afrika

Kyautata Musayar Al’Adu Zai Toshe Duk Wata Kafa Ta Baraka Tsakanin Sin Da Afrika

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.