ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Na Yin Tasiri Mai Yakini A Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Attendees take photographs of themselves in front of a banner at the COP27 climate conference in Sharm El-Sheikh, Egypt, on Sunday, Nov. 6, 2022. Disagreements over who should pay for the harm done by climate-driven extreme weather events will be at the heart of discussions at COP27, the first to be held in Africa since 2016. Photographer: Islam Safwat/Bloomberg

Attendees take photographs of themselves in front of a banner at the COP27 climate conference in Sharm El-Sheikh, Egypt, on Sunday, Nov. 6, 2022. Disagreements over who should pay for the harm done by climate-driven extreme weather events will be at the heart of discussions at COP27, the first to be held in Africa since 2016. Photographer: Islam Safwat/Bloomberg

Wasu abubuwa guda 2 da suka faru a kwanan baya sun nuna hadin gwiwar kut da kut da kasashen Afirka da kasar Sin suke yi a fannin kula da harkokin kasa da kasa.

Daya shi ne yadda Afirka da Sin suka hada kai wajen tabbatar da an zartas da kudurin kafa asusun biyan diya ga kasashe masu tasowa, wadanda suka samu hasara sakamakon bala’un da sauyawar yanayin duniya ke haddasawa, a taron bangarorin da suka sanya hannu kan yarjejeniyar tinkarar sauyawar yanayi ta MDD na COP27, wanda ya kasance wata babbar nasarar da kasashe masu tasowa suka cimma a kokarinsu na muhawara da kasashe masu sukuni.

  • Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Taron MDD Da Sin Kan Huldar Kasa Da Kasa Game Da Binciken Sararin Samaniya

Dayan kuwa shi ne yadda kasar Sin ta nuna goyon baya ga kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU kan batun halartarta kungiyar kasashe masu karfin tattalin arziki ta G20, inda a wajen taron kolin G20 na 17 da ya kammala a kwanakin baya, kasar Sin ta zama mambar kungiyar G20 ta farko da ta nuna goyon baya ga kungiyar AU a fili.

ADVERTISEMENT

Na san wadannan abubuwa za su sanya ku yin tambayar cewa, mene ne ya sa har kullum kasashen Afirka da kasar Sin ke hadin kai da juna, yayin da suke kula da al’amuran kasa da kasa?

A gani na, dalili shi ne, kasar Sin da kasashen Afirka suna da tunani iri daya. Da farko, dukkansu na son tabbatar da yanayi na adalci a duniya. Saboda sun taba shan wahala sakamakon tsare-tsaren duniya da kasashen yammacin duniya ke jagoranta, inda a kan yi musu danniya a fannonin siyasa da tattalin arziki. Wannan niyyar bai daya, ta zama wani tushe mai karfi ga hadin gwiwar Sin da Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Idan mun dauki maganar tinkarar sauyawar yanayin duniya a matsayin misali. Kasashen yamma sun bukaci kasashen Afirka da su dauki nauyin rage fitar da iska mai dumama yanayi iri daya da nasu, ko da yake hakikanin adadin iskar da kasashen Afirka ke fitarwa bai wuce kaso 3 bisa dari na jimillar adadin dukkanin duniya ba. Sai dai a nata bangare, kasar Sin ta jaddada bukatar daukar nauyi mabanbanta tsakanin kasashe masu sukuni da masu tasowa.

Sa’an nan kasar Sin ita ma tana fuskantar matsin lambar da kasashen yamma suke yi mata, inda suke neman soke matsayin kasar na wata kasa mai tasowa, don dora mata matukar nauyi na rage fitar da hayaki da samar da kudi. Duk da haka, kasashen Afirka sun yaba wa kasar Sin kan yadda take kokarin samar da gudunmowa ga aikin raya makamashi masu tsabta a duniya, kana sun bukaci kasashen yamma da su dauki karin nauyi, bisa yadda suka dade suna fitar da dimbin hayaki mai guba cikin shekaru 200 da suka wuce.

Na biyu shi ne, kasashen Afirka da kasar Sin suna dora matukar muhimmanci kan abu daya, wato neman ci gaba. Sabanin yadda wasu kasashen yamma suke dora muhimmanci kan kare ikonsu na yin babakere a duniya, da takara da wasu kasashe, Sin da Afirka na ta kokarin neman hanyar raya kasa. Misali, a taron G20 na wannan karo, kasashen yamma sun fi mai da hankali kan batun dora wa kasar Rasha taken “kasa mai kai hari ga saura”, yayin da a nasu bangare, shugabannin kasashen Afirka da Sin ke nanata kalmomi irinsu “hadin kai”, da “raya kasa”, da “amfanin kowa”, da dai sauransu, a cikin jawaban da suka gabatar.

Ya kamata mu tuna da cewa, yawan al’ummar kasar Sin da ta kasashen Afirka ya kai fiye da kashi 35% na daukacin al’ummar duniya. Duk wadannan mutane masu yawa haka, suna son tabbatar da yanayin adalci a duniya, da kokarin hadin gwiwa don kare moriyar kowa, wannan abun alheri ne ga daukacin ‘yan Adam, wanda ke samar da tasiri mai yakini ga duniyarmu ta wannan zamani. (Bello Wang)

 

 

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Kyautata Musayar Al’Adu Zai Toshe Duk Wata Kafa Ta Baraka Tsakanin Sin Da Afrika

Kyautata Musayar Al’Adu Zai Toshe Duk Wata Kafa Ta Baraka Tsakanin Sin Da Afrika

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.