Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta ce yanzu haka Sin da kungiyar tarayyar Turai EU, na tattaunawa dangane da kafa tsarin tuntuba game da batutuwan cinikayya da zuba jari, kuma za su ci gaba da gudanar da shawarwari.
A yau Asabar, kakakin ma’aikatar cinikayyar Sin ya bayyana yadda Sin ke wanzar da tattaunawa tare da EU. Ya bayyana hakan ne yayin da yake amsa tambayar da aka yi masa, dangane da mahawarar da ta gudana a jiya Juma’a, karkashin dandalin manyan jami’an hukumar gudanar kungiyar EU game da alakar EU da kasar Sin.
Jami’in ya ce Sin da EU, muhimman abokan huldar tattalin arziki da cinikayya ne dake cudanya bisa daidaito, da cimma moriyar juna, kuma Sin na fatan bangaren EU zai rungumi dokokin kungiyar cinikayya ta duniya ko WTO, zai martaba gogayyar ciniki cikin ‘yanci da adalci, tare da nuna matukar adawa da kariyar cinikayya da aiwatar matakan kashin kai.Kazalika, kakakin ya bayyana fatan cewa, EU za ta yi aiki tare da Sin wajen aiwatar da kudurorin da shugabannin sassan biyu suka cimma, da magance bambance-bambance, da sabani, ta hanyar shawarwari da tuntubar juna, da goyon bayan bunkasar dangantakar tattalin arziki da cinikayya mai daidaito da karko tsakanin Sin da EU. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post