Dakarun Rundunar Sojojin Nijeriya tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro sun kashe ’yan ta’adda takwas a ranar Alhamis, tare da ƙwato bindigogi da babura yayin wani samame da suka yi a Ƙaramar Hukumar Bakori.
Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji ta 17 Birget, Abayomi Adisa, ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Katsina ranar Alhamis.
Adisa ya ce an gudanar da aikin ne bayan samun sahihan bayanan sirri cewa wasu ’yan ta’adda masu biyayya ga fitaccen shugaban ’yan bindiga, Idi Abasu Aiki, na shirin tare hanyar Kakumi–Guga domin kai hari kan matafiya dake kan hanyar.
A cewarsa, dakarun sun yi gaggawar ɗaukar mataki ta hanyar kafa kwanton bauna a kan hanyar da ake sa ran ’yan ta’addan za su bi, lamarin da ya kai ga samun nasarar dakile harin tare da kashe takwas daga cikinsu.
Baya ga kashe waɗanda ake zargin, jami’an tsaron sun kuma ƙwato bindigogi kirar AK-47 guda biyu da babura guda biyar da ake zargin ’yan ta’addan ke amfani da su wajen gudanar da hare-harensu.














