ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Ci Gaba Da Taka Rawa A Fannin Makamashi Mai Tsafta A Duniya

by CGTN Hausa
3 years ago
Makamashi

Daya daga cikin bangarori da duniya ta karkata a halin yanzu shi ne, hanyoyin samar da makamashi mai tsafta, don biyan bukatun al’umma, da ma raya tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, a kokarin da ake yi na yaki da matsalar sauyin yanayi dake gurbata muhallin duniyarmu.

Yayin da wasu kasashe ke ci gaba da amfani da makamashin kwal, gas ko man fetur don biyan bukatunsu na makamashi, wadanda masana ke cewa suna gurbata muhalli, ita kuwa kasar Sin ta yi nisa wajen cimma manyan nasarori a fannin makamashi mai tsafta a duniya.

  • Xi Ya Aika Wa Shugaban Nauru Sakon Murnar Ranar Samun ’Yancin Kai Ta Nauru
  • Binciken Kwatsam Da Amurka Ta Yi Kan Kamfanin Sin Ya Janyo Sanyin Gwiwa Game Da Kasuwar Amurka

Babban manazarci a hukumar kula da makamashi ta duniya (IEA) Heymi Bahar ya bayyana cewa, nasarorin da kasar Sin ta samu a fannin makamashin da ake iya sabuntawa, abin misali ne ga daukacin duniya.

ADVERTISEMENT

A cikin rahoton shekara-shekara da hukumar IEA ta fitar a farkon wannan wata, ta lura cewa, duniya ta samu karin kashi 50 cikin 100 na karfin makamashin da ake iya sabuntawa a cikin shekarar 2023, fiye da na shekarar 2022, inda ta yi hasashen za a samu saurin bunkasuwa a shekaru biyar masu zuwa.

A fannin ci gaban da aka samu a fannin samar da wutar lantarki bisa hasken rana, kasar Sin ita kadai ta girka kusan na’urorin samar da wutar lantarki bisa haske da suka kai karfin 220GW, daidai da sauran kasashen duniya, wanda ya ninka saurinta a cikin shekara guda. Wannan ya kara nuna cewa, kasar Sin tana cika dukkan alkawuran da ta yi game da matakanta na raya makamashi mai tsafta, a kokarin da take yi na sauke nauyin dake bisa wuyanta a bangaren yaki da matsalar sauyin yanayin duniyarmu.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Masana na cewa, kasar Sin ta yi fice a matsayin kasar da ta fi kowace kasa a duniya samar da na’urorin samar da wutar lantarki bisa hasken rana na PV a duniya, inda ta ba da gudummawar kusan kashi 80 cikin 100 na masana’antun dake samar da irin wadannan na’urori a duniya.

Don haka, wannan wata dama ce ga kasashen duniya, musamman kasashe masu tasowa su koyi dabaru, da fasahohin da Sin din ta yi amfani da su wajen cimma wadannan nasarori, ta yadda ko dai su amfana da wadannan na’urori ko kuma su samar da wadanda za su dace da yanayin kasashensu. (Ibrahim Yaya)

Makamashi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Sin: Taimakawa Lardin Hunan Don Habaka Hadin Gwiwa Da Afirka

Sin: Taimakawa Lardin Hunan Don Habaka Hadin Gwiwa Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.