A yau Juma’a mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce manufar kasar Sin ta kawar da daukacin harajin kwastam kan hajojin kasashen Afirka 53 masu huldar diflomasiyya da Sin, sabuwar kafa ce ta samar da damar fitar da hajojin nahiyar Afirka zuwa waje.
Kazalika manufar muhimmin misali ne na aniyar kasar Sin ta kiyaye kudurorin da shugaban kasar Xi Jinping ya gabatar, wadanda suka kunshi gaskiya, da cimma sakamako na hakika, da kawance, da amincewa juna, da burin cimma moriyar bai daya tare da kasashen Afirka.
Jami’ar ta ce, Sin na farin cikin shigar karin hajojin musamman masu inganci na Afirka cikin kasuwar kasar, kuma za ta aiwatar da manufar kawar da dukkanin harajin, da kyautata matakan shigar da hajojin Afirka masu inganci, ta yadda al’ummun sassan biyu za su samu karin damar hada-hada da cimma gajiya.
Rahotanni na cewa, babbar hukumar kwastam ta kasar Sin ko GAC, ta ce tun daga ranar 20 ga watan Yulin wannan shekara, Sin za ta bayar da cikakkiyar damar shigar da waken kofi da ya cika ka’idoji daga dukkanin kasashen Afirka masu huldar diflomasiyya da Sin zuwa kasuwar kasar.
Tuni kuma wannan sanarwa ta samu matukar karbuwa daga kasashen Afirka masu nasaba da batun. (Saminu Alhassan)














