Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau 13 ga wata cewa, a karo na 36 a jere, ministan harkokin wajen Sin ya zabi nahiyar Afirka a matsayin zangon farko na ziyara a sabuwar shekara, lamarin da ya shaida cewa, jama’ar kasar Sin sun sada zumunta mai zurfi da jama’ar nahiyar Afirka. Kuma kasar Sin tana son kasashen Afirka su rike damar ci gabanta wajen cimma burin zamanintar da kansu.
Game da yadda Amurka ta ce tana maida hankali ga ayyukan soja a kasar Iran, Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan Iran wajen tabbatar da zaman lafiya a kasar, kuma ba ta amince da tsoma baki cikin harkokin cikin gidan sauran kasashe da yin amfani da karfin tuwo domin daidaita huldar dake tsakanin kasa da kasa ba.
Game da tattaunawar ministocin kudi na kasashe membobin kungiyar G7 kan rage amfani da ma’adinan da suke da wuyar samu na kasar Sin, Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin na tsaya tsayin daka kan manufar tabbatar da samar da kayayyakin ma’adinai da tabbatar da ingancinsu a duniya. (Zainab Zhang)














Discussion about this post