Memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi ya zanta da ministan harkokin wajen kasar Somaliya Abdisalan Abdi Ali Dhaay ta wayar tarho.
A yayin zantawarsu, sun sake tabbatar da tushen kare dangantakar abokantaka a tsakanin kasar Sin da kasar Somaliya bisa manyan tsare-tsare, da kuma goyon baya ga juna kan harkokin dake shafar muhimmiyar moriyar kasashen biyu, sun kuma yi maraba da samun bunkasar dangantaka a tsakanin kasashen biyu. Haka kuma, sun cimma matsayi daya kan zurfafa fahimtar siyasa da karfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata, tare da jaddada cewa, kasashen biyu za su hada kansu, domin kiyaye ’yancin kai da dunkulewar kasashensu, da kuma kare ka’idar daina tsoma baki cikin harkokin gida na kasashe.
Bugu da kari, kasar Sin ta sake jaddada goyon bayanta ga kasar Somaliya domin kare ’yancin kan kasa, kuma, ba wanda zai iya raba yankin Somaliland daga kasar Somaliya ba.
A nata bangare kuma, kasar Somaliya ta jaddada goyon bayanta kan manufar kasar Sin daya tak a duniya, da kuma dukkanin kokarin da gwamnatin kasar Sin ke yi domin cimma burin dunkulewar kasar. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post