Mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng, ya bayyana a yau Talata cewa, kasarsa na matukar goyon bayan manyan kamfanonin kasa da kasa wajen zuba jari da yin kasuwanci, har ma da habaka da samun ci gaba cikin aminci a kasar.
Han Zheng ya bayyana haka ne lokacin da yake jawabi ga taro na 7 na manyan kamfanonin kasa da kasa a birnin Qingdao na lardin Shandong da ke gabashin kasar Sin.
Ya ce kokari da Sin take yi na neman ci gaba mai inganci da fadada bude kofarta, ya samar da wani katafaren dandali na ci gaban kamfanonin kasa da kasa.
Ya kuma bayyana fatan manyan kamfanonin na kasa da kasa za su samar da kayayyaki da hidimomi masu matukar inganci da zurfafa hadin gwiwa da Sin a bangaren ayyukan masana’antu da kuma aiki tare da ita wajen gina sabon muhallin ci gaba ta hanyar kirkire kirkire wanda zai zama mai juriya da damarmaki da karfin takara. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post