A yau Litinin shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jinjinawa kasar Pakistan bisa kokarinta na shiga tsakani domin tabbatar da dawo da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.
Shugaba Xi ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da firaministan kasar Pakistan Shehbaz Sharif.Shugaba Xi ya kara da cewa, kamata ya yi Sin da Pakistan su gaggauta gina kawancen al’ummunsu mai makomar bai daya a sabon zamani, su kuma cimma karin nasarori bisa hadin gwiwarsu a dukkanin fannoni.
Daga nan sai ya yi kira ga sassan biyu, da su samar da karin gajiya ga al’ummunsu, da bayar da gudummawar ingiza zaman lafiya da daidaito a yankinsu, tare da samar da misali mai kyau a fannin gina al’umma mai makomar bai daya tsakanin kasashe makwafta.
A nasa bangare kuwa, Sharif ya ce, kasarsa na godewa Sin, bisa tallafinta ga Pakistan dangane da aikin shiga tsakanin Amurka da Iran, yana mai cewa, shawarwari hudu da shugaba Xi ya gabatar game da yanayin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya, sun samar da jagoranci ga burin cimma zaman lafiya. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post