Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Laraba 27 ga Mayu da Alhamis 28 ga Mayu, 2026 a matsayin ranakun hutu domin bikin Sallar Layya (Eid al-Adha).
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar ma’aikatar, Magdalene Ajani, ta fitar ranar Litinin.
Sanarwar ta ce matakin na nuna girmamawar gwamnatin tarayya ga addini da al’adun na miliyoyin Musulmai a Nijeriya da ma duniya baki ɗaya da ke gudanar da bikin babbar Sallah.
Olubunmi Tunji-Ojo ya taya al’ummar Musulmi murnar bikin, yana mai bayyana bikin Sallar Layya a matsayin lokaci mai cike da ma’ana ta sadaukarwa, da biyayya ga Allah da kuma tausayi ga bil’adama.
Ministan ya kuma buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi amfani da lokacin hutun wajen addu’o’i da tunani domin zaman lafiya, da tsaro da ci gaban ƙasa, tare da kira ga jama’a su rungumi ruhin haɗin kai da zaman lafiya yayin gudanar da bukukuwan Sallah.















Discussion about this post