A yau Talata shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin, zai fara ziyarar aiki a kasar Sin. Da yake amsa tambayoyi a taron manema labarai na yau da kullum, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun, ya bayyana cewa, Sin tana maraba da ziyarar aiki da shugaba Putin zai gudanar a kasar. A cewarsa Sin da Rasha abokan hadin gwiwa ne bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a sabon zamani. Ya ce a yayin ziyarar shugaba Putin a kasar Sin, shugabannin kasashen biyu za su yi musayar ra’ayoyi kan dangantakarsu da hadin gwiwarsu a fannoni daban daban, da kuma batutuwan kasa da kasa da na shiyya-shiyya dake jawo hankulansu duka.
A wani rahoton kuma, a ‘yan kwanakin nan, majalisun kula da Ilimi na bangarorin biyu karkashin kwamitin abokantaka da zaman lafiya da ci gaba tsakanin Sin da Rasha sun gudanar da wani binciken jin ra’ayoyi mai taken “Abokantakar Matasan Sin da Rasha da Musayar Al’adu Tsakaninsu” ga matasa masu shekaru 18 zuwa 35 na kasashen biyu.
Sakamakon ya nuna cewa, sama da kashi tamanin cikin dari na matasan Sin da Rasha na ganin cewa, dangantakar Sin da Rasha ta abokantaka ce. Kuma dangane da haka, Guo Jiakun ya bayyana cewa, sun yi imanin cewa, karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping da shugaba Putin, dadaddiyar abokantakar Sin da Rasha za ta kara wanzuwa a zukatan jama’a, matasan kasashen biyu kuma za su hada karfi da karfe, domin samar da kuzari ga cikakkiyar dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Rasha a sabon zamani. (Bilkisu Xin)














Discussion about this post