Sin ta bayyana matukar adawa da matakin Amurka na girke makamai masu linzami masu cin matsakaicin zango a kasashen AsiyaKakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun ne ya bayyana haka a yau Juma’a yayin taron manema labarai na yau da kullum, inda ya bukaci Amurka da Japan su gyara kuskurensu.
Rahotanni daga kafafen yada labarai sun ruwaito cewa, rundunar sojin Amurka na shirin girke makamai masu linzami da ke cin matsakaicin zango a Japan, tsakanin watan Yuni da Satumba, domin atisayen soji na hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.
Kana bayan atisayen, za a kai makaman sansanin sojin Amurka da ke Japan. (Fa’iza Mustapha)
ADVERTISEMENT
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/















Discussion about this post