Gwamnatin Jihar Katsina na shirin samar da tsarin kula da masu cutar daji a ƙoƙarin da take na bunƙasa kula da lafiya.
Ana saran aikin samar da cibiyar zai amfanar da al’ummar jihar har ma da marasa lafiya daga faɗin Nijeriya da kuma ƙasashen maƙwabta.
Gwamna Dikko Umar Raɗɗa ya faɗi haka yayin da yake gabatar da jawabi ga wata tawaga daga ƙasar Jamus a gidan gwamnati da ke Katsina.
Gwamnan ya ce wannan cigaba zai ɗaga matsayin Jihar Katsina na zama gaba wajen samar da kayan aiki da kula da masu fama da cutar kansa.
Gwamna Raɗɗa ya yaba wa ma’aikatar kula da harkokin lafiya ta jihar bisa haɗin guiwa da kamfanin ƙasar Jamus, yana mai cewa irin wannan haɗin guiwa hanya ce ta bunƙasa harkokin kiwon lafiya.
Gwamna ya bayyana fatan cewa haɗin guiwar za ta ci gaba da sanya injina da kayan aiki tare da ci gaba da horas da ma’aikatan lafiya.
Ya bayyana cewa a halin da ake ciki wasu ma’aikatan lafiya na samun horo a ƙasar Jamus, yayin da saura ke karɓar horon ta yanar gizo kan yadda za a yi amfani da mashinan.
A nashi jawabi, Manajan Daraktan Kamfanin mai kula da yankin gabas maso yamma na Afrika, Ansu Dukuray ya ce a kowacce shekara kimanin mutane miliyan 20 ke mutuwa a faɗin duniya sakamakon cutar kansa.
Ya ce kamar yadda ƙididdiga ya nuna a kowacce rana mutane dubu 26 ke mutuwa sakamakon cutar.
Dukuray ya yi gargaɗin cewa muddin ba a ɗauki matakin da ya kamata ba, nan da shekara 2050 alƙalumman mutanen da za su rasa rayukansu zai iya ƙaruwa zuwa miliyan 35 kowace shekara.
Shi ma kwamishinan kula da harkokin lafiya na jihar, Alhaji Musa Adamu Funtua ya ce tsarin ya yi daidai da ƙudirin gwamnati na gina goben jihar.















Discussion about this post