Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya ce, bangaren Sin ya nuna adawa da takunkumi da ake kakabawa daga bangare daya ba tare da wata hujja a cikin dokokin kasa da kasa, ko izini daga kwamitin sulhu na MDD ba.
Guo ya bayyana hakan ne yayin da yake mai da martani ga batun kakaba takunkumi ga kamfanonin Sin guda uku da Amurka ta yi bisa hujjar taimaka wa Iran ta fuskar ayyukan soja, a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Litinin.
Game da yanayin da ake ciki a Iran, Guo ya bayyana cewa, bangaren Sin ya riga ya nuna matsayinsa sau da dama, babban aikin da ya fi bukatar gaggawa shi ne yin iyakacin kokarin hana sake barkewar yaki, maimakon amfani da rikicin wajen yi wa sauran kasashe batanci.
Bugu da kari, game da babban taron kiwon lafiya na duniya karo na 79 da ke tafe, Guo ya bayyana cewa, domin tabbatar da manufar kasar Sin daya tak da kuma kare mutuncin kudurorin da suka shafi babban taron MDD da kuma babban taron kiwon lafiya na duniya, Sin ta yanke shawarar kin amincewa yankin Taiwan ya halarci taron na wannan shekarar.
Duk wani yunkuri na karya ka’idar kasar Sin daya tak da kuma dabara ta siyasa da aka bullo da ita bisa batun Taiwan, ba zai kai gaci ba. (Safiyah Ma)















Discussion about this post