‘Yansanda Sun Kama Mutane 11 Da Ake Zargi ‘Yan Ƙungiyar Asiri Ne Kan Kashe Mutane Takwas A Benuwe
Rundunar ‘Yansandan Jihar Benuwe ta kama mutane 11 da ake zargi ‘yan ƙungiyar asiri ne wadanda kuma ke da hannu dangane da kashe mutane takwas a wani hari da aka kai da sanyin safiya a Makurdi.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Udeme Edet, ta tabbatar da kamen cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin a Makurdi, inda ta ce an tura jami’ai zuwa wurin nan take bayan samun kiran gaggawa.
A cewar sanarwar, “A ranar 11 ga watan mayun, 2026 da misalin ƙarfe 2:30 na dare, wani mai gida a Titin Aliade, High Level, Makurdi, ya kira wayar gaggawa domin sanar da cewa wasu mutane ɗauke da makamai sun shiga gidansa, sun fito da wasu matasa daga ɗakinsu sannan suka harbe su.”
Ta ƙara da cewa, binciken farko ya nuna harin na da alaƙa da rikicin ƙungiyar asiri, kuma ana zargin wani jagoran wata ƙungiya mai suna “Odinaka” ne ya jagoranci harin, wanda yanzu haka, ana nemansa ruwa a jallo.















Discussion about this post