Tawagar kasar Sin mai halartar babban taro karo na 79 na majalisar zartarwa ta hukumar lafiya ta duniya WHO, ta gudanar da taron manema labarai a jiya Lahadi 17 ga watan nan a birnin Geneva na kasar Switzerland.
Yayin zaman, a matsayinsa na shugaban tawagar Sin, babban daraktan hukumar kiwon lafiya ta Sin Lei Haichao, ya yi bayani game da ci gaban da Sin ta samu a fannin aiwatar da sabuwar manufar bunkasa kiwon lafiyar jama’a.
Inda ya ce Sin a shirye take ta raba kwarewarta, da fasahohinta a fannin jagorancin kiwon lafiyar al’umma tare da sauran sassan kasa da kasa, kana tana da burin yin aiki tukuru wajen gudanar da hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya tsakanin sassan dake aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da ci gaba da aikewa da tawagogin kiwon lafiya na dindindin zuwa kasashe masu tasowa.
Lei Haichao, ya kara da cewa a halin da ake ciki, akwai tawagogin kiwon lafiya na Sin sama da 60 dake aiki a kasashen ketare, wadanda ke taka muhimmiyar rawa a kasashe irin na Afirka da Latin Amurka, ba a bangaren samar da hidimomin kiwon lafiya kadai ba, har ma da yada fasahohin zamani, da yayata kwarewa da jami’an kiwon lafiya na kasar Sin suka samu, da kyankyashe tarin ma’aikata masu hazaka da ake bukata a yankunan.
Wannan a cewar jami’in, muhimmiyar gudunmawa ce da Sin ta samar ga sassan kasa da kasa, yayin da take kokarin warware nata batutunwa na kiwon lafiya.Taron majalisar zartarwar hukumar lafiya ta duniya WHO karo na 79, zai gudana ne tun daga yau Litinin 18 zuwa Asabar 23 ga watan nan na Mayu, bisa muhawara mai jigon “sauya tsarin kiwon lafiyar duniya da raba nauyin hakan.” (Saminu Alhasssan)















Discussion about this post