An gudanar da bikin sanya hannu kan takardar mika kayayyakin agajin gaggawa na jin kai da Sin ta bai wa Iran a hedkwatar kungiyar agaji ta Red Crescent ta Iran a birnin Tehran ranar 15 ga watan Afrilu, inda jakadan Sin a Iran Cong Peiwu da shugaban kungiyar Red Crescent ta Iran Pirhossein Kolivand suka halarta.
Cong Peiwu ya bayyana cewa, bangaren Sin yana tausayin al’ummar Iran a ko da yaushe, kuma ba da agajin gaggawa na jin kai ga Iran a wannan karo aiki ne mai kyau na aiwatar da manufar kyakkyawar makomar bil-Adam ta bai daya da kuma sauke nauyi dake rataye a wuyan kasa da kasa a bangaren jin kai.
Tun bayan barkewar rikicin, bangaren Sin ya himmatu wajen maido da zaman lafiya a yankin da kuma kawo karshen rikici. Haka kuma bangaren Sin zai ci gaba da hadin gwiwa da al’ummar kasa da kasa, don kwantar da hankali a Gabas ta Tsakiya cikin gaggawa.
Yayin babban taron MDD kan ikon mambobin dindindin na kwamitin sulhu na kada kuri’ar kin amincewa da wani kuduri da ya gudana a jiya 16 ga watan, wakilin dindindin Sin a MDD Fu Cong, ya bayyana cewa, rashin amincewa da daftarin kudurin da ya shafi mashigin Hormuz da Sin ta yi a ranar 7 ga wata a kwamitin, ya kare adalci na kasa da kasa, da kare manufa da ka’idojin yarjejeniyar MDD, kuma ya hana kara tsananta rikicin, ya kuma haifar da yanayi mai kyau na cimma tsagaita wuta na wucin gadi da kuma fara tattaunawa da yin shawarwari. (Amina Xu)














Discussion about this post