Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce Sin na goyon bayan kasar Cuba dangane da kare ikon mulkin kai, da tsaro da muradun ci gabanta.
Mao, ta yi wannan tsokaci ne a yau Laraba, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, bayan da a jiya Talata, yayin taron manyan jami’ai da kwamitin tsaron MDD ya gudanar, ministan harkokin wajen Cuba Bruno Rodriguez, ya soki matakin Amurka na ta’azzar barazanar soji da take yiwa Cuba.Game da hakan, Mao ta ce har kullum, Sin na yayata bukatar martaba ikon mulkin kai, da kare martabar yankunan dukkanin kasashe, tana kuma adawa da amfani da barazana, ko karfi a alakar kasa da kasa, kana Sin na adawa da keta hurumin ikon mulkin kai na sauran kasashe, da tsoma baki cikin harkokinsu na cikin gida ta duk wata hanya.
Jami’ar ta kara da cewa, kamata ya yi kasashen duniya su kiyaye dokokin kasa da kasa, da ka’idojin cudanyar sassan kasa da kasa karkashin tsarin MDD. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post