Jam’iyyar ADC ta buƙaci ‘yan Nijeriya da kada su yanke ƙauna duk da matsalolin tattalin arziki da ƙasar ke fuskanta, yayin da Musulmi a Nijeriya da sassan duniya ke bikin Babbar Sallah.
A cikin saƙon taya murnar Sallah da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta miƙa sakon barka ga al’ummar Musulmi tare da bayyana bikin sallar a matsayin lokaci mai nuna sadaukarwa, imani, biyayya da tausayi.
Jam’iyyar ta amince cewa bikin bana na zuwa ne a daidai lokacin da matsin rayuwa ke ƙaruwa ga ‘yan Nijeriya da dama, inda hauhawar farashin abinci, rashin aikin yi, matsalar tsaro da rashin tabbas a tattalin arziki suka sanya nauyi mai yawa a kan iyalai da dama a faɗin ƙasar.
A cewar ADC, duk da cewa mutane da dama na cikin mawuyacin hali, ya kamata ‘yan ƙasa su ci gaba da yin imani da fata nagari domin samun makoma mafi kyawu ga Nijeriya.















Discussion about this post