Babbar hukumar kwastam ta kasar Sin ta ce kasar ta bude kasuwarta ga gyadar sha zawa ko cashew nut daga kasashen da ke samar da ita a nahiyar Afrika, wadanda ke da huldar diplomasiyya da ita. Amma sai gyadar ta cika sharudan bincike da aminci da tsafta da ake bukata.
An fara ba kasashe masu samar da gyadar sha zawa damar ce a ranar 9 ga watan nan na Yuni. Nahiyar Afrika ita babbar mai samar da gyadar sha zawa a duniya. A baya, kasashen nahiyar kalilan da suka hada da Guinea Bissau da Mozambique da Gambia ne suka samu damar shigar da gyadar cikin kasar Sin.
A cewar hukumar ta kwastam, nazari ya gano cewa kasashen Afrika na fuskanta makamanciyar barazanar cututtuka da kwari da ke da alaka da samar da cashew nut, lamarin da ya ba Sin damar samar da sharudan binciken aminci da tsafta na bai daya ga masu shigar da gyadar sha zawa kasar daga nahiyar Afrika.
Wani jami’in hukumar ya ce sabon tsarin ya kawar da mabambantan tsare-tsaren bincike ga kasashen Afrika da ke son kawo gyadar kasar Sin. Ya ce idan kayayyaki suka cika sharudan da aka gindaya, to za su samu damar shiga kasuwar kasar Sin. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post