Majalisar Dattawa ta sanar da shirin gudanar da zaman gaggawa a ranar 23 ga Yuni, 2026, domin tattauna muhimman batutuwan ƙasa, musamman halin da tsaron kasa ke ciki da sauran matsalolin da ke buƙatar matakin gaggawa daga majalisar.
A cikin wata sanarwa mai ɗauke da ranar 15 ga Yuni, wadda Magatakardar Majalisar Dattawa, Emmanuel Odo, ya sanya wa hannu, an sanar da sanatoci cewa za a dakatar da hutun majalisar na ɗan lokaci domin duba batutuwan da ake ganin suna da muhimmanci ga zaman lafiyar ƙasa da tafiyar da mulki.
Sanarwar ta bayyana cewa an kira zaman gaggawar ne bisa umarnin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.
Za a gudanar da zaman ne ranar Talata, 23 ga Yuni, 2026, da ƙarfe 11:00 na safe a harabar Majalisar Tarayya da ke Abuja.
Ana sa ran sanatoci za su tattauna matsalolin tsaro da suka haɗa da yawaitar hare-haren ’yan bindiga, sace-sacen mutane, da sauran ƙalubalen tsaro da ke addabar sassa daban-daban na ƙasar nan, tare da duba hanyoyin da za a ɗauka domin magance su.














Discussion about this post