Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Amurka ta tsoma baki cikin matakin da Sin ta dauka na kiyaye ikon mulki da mallakar cikakkun yankunanta, tare da adawa da aikin da Sin ta yi na kiyaye ka’idar kasar Sin daya tak, yana cewa hakan bai dace ba ko kadan.
Ya ce kasar Sin na bukatar Amurka da ta daina amfani da batun Taiwan wajen tsoma baki cikin harkokin siyasar cikin gidanta ta, kuma ta daina taimaka wa Taiwan don karfafa abin da take kira da “huldar diplomassiya”.
Guo ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai da aka gudanar yau Alhamis, lokacin da ya mai da martani game da kalamai na rashin dacewa da bangaren Amurka ya yi kan batun “daga” ziyartar Eswatini da shugaban yankin Taiwan Lai Ching-te ya yi.
Bugu da kari, game da halin da ake ciki a duniya a yanzu, Guo ya ce, zabin da ya dace kawai shi ne kasa da kasa su hada gwiwa kuma su taimaka wa juna.
Ya ce Sin na fatan hanzarta cimma ajandar samun ci gaba mai dorewa ta shekarar 2030 ta MDD ta hanyar aiwatar da shawarwarin ci gaban duniya tare da dukkan bangarori. (Safiyah Ma)















Discussion about this post