Alamu na nuna cewa, akwai matukar bukatar, a yi takatsantsan, duba da yadda wasu al’amura suka fara bayyana a yayin da zabukan 2027 ke kara kunnu kai.
Duk da cewa, batun yamutsa hazon siyasar kasar, ba su fara bayyana a zahirance ba, amma wasu ‘yan kasar sun fara bayyana fargabarsu, kan Kasancewar sahihancin hukumar zabe a matsayin ta na mai cin gashin kanta da kuma nauyin da ke a kanta, inda kuma a gefe daya, jami’iyyun kasar, ke ta faman kai komo, domin rike madafun iko.
Lamarin dai, ba wai batun kada kuri’a bane, amma za a gudanar da sahiahi kuma karbabben zabe da ya yi daidai da masu zaben suka zaba.
Amma matukar aka saba hakan, zai janyo jefa rashin yarda da sakamakon zabukan da haifar da rikici a cikin kasar.
Tuni dai, a kasar a ka fara ganin rikicin cikin gida a wasu jami’iyyun kasar, musamman na hakilon samun shugabantar jami’iyyunsu da kuma yadda sauya sheka, ya zama ruwan dare, a tsakanin jami’iyyun.
Hakan ya sanya, jami’iyyun sun yi hannun Riga kan akidar da aka kafa su na tabbatar da ainahin kima da daraja da kuma ginshikin mulkin dimokiradiyya.
Nijeriya dai ta kasance an kafa ta ne, tun a jamhuriya ta farko a kan turbar jami’iyyu da dama, amma kusan za a iya cewa, batun ya sauya ganin yadda kasar ke neman komawa, kan turbar jami’iyyar daya tilo.
Sai dai, an ruwaito shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, a kashin kansa, ya yi watsi da ikirarin cewa, gwamnatin sa, na kokarin yin uwa da makarbiya, na dora turbar siyayar kasar, a matakin mai bin tsarin siyasa daya tilo.
Duk da wannan watsin da Tinubu ya yi na ikirarin, amma jami’iyyun adamwar kasar, sin dage kai da fata, suna ci gaba sukar shugaban da kuma jami’iyyar sa ta APC, kan kokarin su na namaye daukacin fagen siyasar kasar, da kuma mayar da Nijeriya a tsarin kasa, mai bin jami’iyya daya.
Ko ma dai menene batun gaskiya kan wannan musayar yawun a tsakanin ‘yan adawar da kuma bayanin shugaban, amma babban abinda dubawar shi ne akwai bukatar a bayar da damar da za ta bai wa masu ruwa da tsaki kwarin guwair su ma a dama da su, domin a kawar da duk wani shakku a tafiyar da siyasar kasar.
Bugu da kari, a bangaren hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC tana ci gaba Kasancewa, a cikin tsaka mai wuya, musamman duba da cewa, kundin tsarin mulkin kasar, ya dora mata babban nauyin tabbatar da kare kimar tsarin gudanar da sahihi kuma amintacen zaben da kowanne dan kasar, zai yi na’am da shi.
Hakazalika, hukumar ba wai nauyin sanya ido kan zabuka ne kawai, nauyin da ke a kanta ba, dole ne kuma ta tabbatar da ta yi adalci, a tsakanin sauran jami’iyyun adawar kasar.
Kazalika, a gafe daya kuma batun kalubalen samar da kayan gudanar da zabe da matsalar rashin tsaro lamuran nuna bangaranci da batun addini, na daga cikin abubuwan da za su iya taka rawa, a zabukan na 2027.
A bangaren Shari”a kuwa, akwai gaganurmar gudunmawar da za ta taka, musamman wajen yanke hukunci, a cikin lokaci a kutunan da ke karbar korafin zabuka, musamman duba da yadda a wasu Shari’un baya, ake zargin kotun, da jan kafa, wajen yanke hukunci a kan lokaci da kuma yanke hukunci, na wasu shari’un zabukan da ke da matukar sarkakiya.
A saboda haka, ya zama wajibi a bangaren Shari’a, a tabbatar da an yi gaskiya wajen yanke hukunci, musamman domin alummar kasar, su ci gaba ganin kimar bangaren ba Shari’a da kuma aminta da bangaren.
Kazalika, suma masu ruwa da tsaki a fannin siyasar kasar, akwai rawar da za su iya takawa na kiyaye sharudda da ka’idojin zabe musamman wajen kaucewa yiwa juna habaici da furta kalaman da zai iya tayar da zaune tsaye, lokacin zabukan da kuma bayan sa.
A bangaren jami’iyyun kasar, suma ya zama wajibi, su tabbatar da suna gudanar da siyasar su ta cikin gida, a cikin yin da’a da gujewa aikata ayyukan da za su iya janyo yamutsa hazon siyasar kasar.
Ita kuwa hukumar zabe ta kasa INEC, ita na ya zama wajibi ta tabbatar da ta yi gaskiya wajen gudanar da ayyukan ta, musamman a bangaren yiwa ‘yan kasar da suka kai munzalin jefa kuri’a, domin su ma, a yi masu rijista da tattara sakamakon zabe tare da kuma yin amfani da fasahar kimiyyar zamani wajen gudanar da zabukan.
Hakazalika, a bangaren ‘yan kasar, suma akwai nauyi a kansu, wajen fitowa su kada kuri’unsu.
Har yanzu, lokaci bai kure wa Nijeriya ba, musamman, wajen karfafa ginshikin turbar dimokiradiyyar kasar, kafin zuwan lokacin gudanar da zabukan na 2027.















Discussion about this post