Jami’an Rundunar ‘Yansandan Nijeriya, ta sashen leƙen asirinta na FID-STS, sun kama wasu mutane huɗu da ake zargin ‘yan bindiga ne tare da kwato bindigogi AK-47 guda huɗu da harsasai 80.
An kama waɗanda ake zargin — Abdumumini Abubakar mai shekaru 40, Maikano Gambo mai shekaru 47, Saleh Thompson mai shekaru 47, da Oyonyi Odango mai shekaru 40 — a ranar 7 ga Maris, 2026, a Tayu da ke ƙaramar hukumar Sanga a Jihar Kaduna, bayan samun sahihan bayanan sirri.
Kakakin rundunar ‘yansanda, Anthony Okon Placid, ya ce kayayyakin da aka kwato daga hannun waɗanda ake zargin sun haɗa da bindigogi AK-47 guda huɗu tare daharsasai 80, da kuma wata bindiga ƙirar gida tare da harsasai 20.
Ya kuma bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin suna da alaƙa da ayyukan ‘yan bindiga da sauran munanan laifuka masu tashin hankali a yankin.
‘Yansandan sun ƙara da cewa, ana ci gaba da bincike domin kamo sauran wadanda suka tsere.















Discussion about this post