• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Goyi Bayan Kudurin Kwamitin Tsaron MDD Na Sake Gaggauta Duba Yiwuwar Amincewa Da Bukatar Falasdinu Ta Zama Mamba A MDD

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Goyi Bayan Kudurin Kwamitin Tsaron MDD Na Sake Gaggauta Duba Yiwuwar Amincewa Da Bukatar Falasdinu Ta Zama Mamba A MDD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin ta goyi bayan kudurin kwamitin tsaron MDD, na sake gaggauta duba yiwuwar amincewa da bukatar Falasdinu, ta zama mamba a MDD. Da yake tabbatar da hakan cikin jawabin da ya gabatar a jiya Jumma’a, yayin zaman gaggawa na babban taron MDD karo na 10, wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Fu Cong, ya jaddada bukatar baiwa Falasdinu matsayin cikakkiyar mamba a MDD.

Fu Cong ya ce “Ya kamata falasdinu ta samu matsayi guda da Isra’ila, kuma nauyi ne a wuyan sassan kasa da kasa, su goyi baya, da ingiza matakan kafuwar kasar Falasdinu mai cin gashin kai, don tabbatar da an aiwatar da tsarin warware matsalar yankin ta hanyar kafa kasashe biyu, da wanzar da zaman lafiya mai dorewa a gabas ta tsakiya”

  • CMG Ta Zanta Da Firaministan Kasar Hungary
  • Xi Jinping Ya Halarci Bikin Ban Kwana Da Firaministan Hungary Ya Shirya Masa

Game da yanayin da ake ciki a baya bayan nan, Fu ya bayyana rashin jin dadi, bisa yadda Amurka ta ki amincewa da kudurin da aka gabatar na baiwa Falasdinu damar zama cikakkiyar mamba a MDD, yayin jefa kuri’un da aka kada a zauren kwamitin tsaron MDD a ranar 18 ga watan Afrilun da ya shude.

Jami’in ya soki lamirin Amurka, bisa yadda ta yi amfani da matsayin ta na mai kujerar naki, wajen dakile damar tarihi ta sauya rashin adalcin da aka yiwa Falasdinawa, yana mai cewa, “matakin ya saba da nauyin dake wuyan wata kasa babba.”

Zaman taron gaggawa na babban taron MDD, bisa babban rinjaye, ya zartas da kudurin dake kara jaddada hakkin al’ummar Falasdinawa na cin gashin kai, da tabbatar da dacewar Falasdinu, na zama cikakkiyar mamba a MDD, da shawartar kwamitin tsaron ya sake duba bukatar ta Falasdinu. (Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarkakkiyar Zargin Da Gwamnatin Abba Ke Wa Ganduje

Next Post

Amfanin Karas 10 Ga Lafiyar Dan’adam

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

7 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

8 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

9 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

10 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

11 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

12 hours ago
Next Post
Amfanin Karas 10 Ga Lafiyar Dan’adam

Amfanin Karas 10 Ga Lafiyar Dan'adam

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.