A yau Laraba ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya amsa tambayoyin da aka yi masa, game da taron musamman na kungiyar tarayyar Afirka AU dangane da barkewar cutar Ebola, wanda ya gudana a jiya Talata ta kafar bidiyo, inda ya ce muhimmiyar mahangar shugaban kasar Sin Xi Jinping, ta gina al’ummar duniya mai makomar bai daya, ta tanadi gina tsarin kiwon lafiya na dukkanin bil’adama, da tsara tafarkin hadin gwiwar kasa da kasa, don yaki da barkewar cutar Ebola.
Ya ce har kullum, Sin da kasashen Afirka suna kasancewa al’umma guda mai makomar bai daya.
Kana kasar Sin ta samar da tallafin jin kai na gaggawa ga jamhuriyar dimokaradiyyar Congo DRC da kungiyar AU, ta kuma aike da tawagar kwararru zuwa DRC, kunshe da jami’an kiwon lafiya kusan 1000, wanda ke yaki da cutar kafada-da-kafada da mutanen nahiyar Afirka. Kazalika, Lin ya ce Sin za ta aiwatar da shirin hadin gwiwa na inganta kiwon lafiya, karkashin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, da samar da tallafi iya karfinta don shawo kan barkewar cutar ta Ebola.
Har ila yau, Sin na kira ga sassan kasa da kasa da su karfafa goyon bayansu, da hadin gwiwa wajen taimakawa nahiyar Afirka cimma nasarar murkushe annobar cikin sauri. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post