Babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta Sin, kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi bayani game da ayyukan hadin gwiwa a tsakanin yankunan gabashi da yammacin kasar, inda ya ce a cikin shekaru 30 da fara aiwatar da su, an sa kaimi ga kawar da talauci, da samun ci gaban yankunan kasar da sauran fannoni, wanda hakan ya shaida fifikon tsarin siyasa na jam’iyyar Kwaminis ta Sin, da kuma tsarin gurguzu na kasar baki daya.
Xi Jinping ya jaddada cewa, shekarar bana, ita ce ta farko a aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15, kana shekara ta farko da aka fara gudanar da ayyukan taimakawa juna a kasar.
Ya ce ya kamata a yi amfani da fasahohin da aka samu daga hadin gwiwa tsakanin lardin Fujian da jihar Ningxia, da kara kyautata tsarin da hanyar yin hadin gwiwa, da fadada fannonin hadin gwiwar, don sa kaimi ga taimakawa juna a fannonin da suke da kwarewa, da musayar kwararru, da fasahohi, da tunani da salon rayuwa, ta yadda za a cimma moriyar juna da bunkasa tare.
An gudanar da taron ayyukan hadin gwiwa a tsakanin yankunan gabashi da yammacin kasar Sin a birnin Yinchuan dake jihar Ningxia ta kasar Sin, a yau Laraba 17 ga wannan wata na Yuni. (Zainab Zhang)














Discussion about this post