Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce Sin a shirye take ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa, wajen warware batun nukiliyar Iran ta hanyoyin siyasa da diflomasiyya, da kuma kare yarjejeniyar kasa da kasa ta hana yaduwar makaman nukiliya, da ingiza zaman lafiya da daidaito a Gabas ta Tsakiya da duniya baki daya.
Mao Ning, ta bayyana hakan ne a Talatar nan, yayin taron manema labarai na yau da kullum da aka saba gudanarwa, lokacin da take amsa tambaya game da batun.
A cewarta, har kullum kasar Sin na goyon bayan matakan shawo kan batun nukiliyar kasar Iran ta lumana, bisa amfani da shawarwari da tattaunawa.
Jami’ar ta kuma yi fatan dukkanin sassan da batun ya shafa, za su yi amfani da damar hakan wajen tattauna hanyoyin shawo kan halin da ake ciki ta la’akari da halastacciyar damuwar sassan da al’amarin ya shafa. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post