Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke hukuncin cewa tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, na da damar tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Mai shari’a Peter Lifu ne, ya yanke hukuncin a ranar Talata bayan an shigar da ƙara domin ƙalubalantar cancantar Jonathan ta sake neman shugabanci.
Wani mutum mai suna Johnmary Jideobi ne, ya shigar da ƙarar, inda ya roƙi kotu ta hana Jonathan tsayawa takara tare da hana INEC karɓar sunansa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa.
Mai ƙarar ya ce Jonathan ya taɓa karɓar rantsuwa sau biyu a matsayin shugaban ƙasa a shekarun 2010 da 2011, don haka bai kamata ya sake tsayawa takara ba bisa kundin tsarin mulkin 1999.
Sai dai kotun ta yi watsi da ƙarar tare da tabbatar da cewa tsofaffin hukunce-hukuncen kotu sun riga sun amince Jonathan zai iya sake neman kujerar shugaban ƙasa.
Alƙalin ya kuma bayyana ƙarar a matsayin ɓata lokaci da amfani da kotu ba daidai ba.
Kotun ta umarci mai ƙarar ya biya Jonathan tarar Naira miliyan 20, sannan ya biya Babban Lauyan Tarayya Naira miliyan ɗaya.















Discussion about this post