Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya bayyana cewa, Sin da kasashen Afirka ’yan uwa ne wadanda ke fuskantar mawuyacin hali tare.
Don haka game da sabon zagayen barkewar cutar Ebola a jamhuriyar demokradiyyar Kongo, gwamnatin Sin ta yanke shawarar mika agajin gaggawa ga kasar, kuma ta tura tawagar kwararrun likitoci zuwa kasar, domin samar da hidimomi da agajin kiwon lafiya.
A lokaci guda kuma, tana bayar da taimako ga kwamitin kungiyar AU, don tallafawa ayyukan kandagarki da shawo kan cutar ta Ebola karkashin cibiyar Afirka CDC.
Lin ya bayyana hakan ne a gun taron manema labarai da aka gudanar a yau Litinin. Kuma a game da shirin kasar Japan na kara habaka hadin gwiwar tsaro tare da kungiyar NATO, Lin ya bayyana cewa, Sin ta nuna matukar damuwa game da matakin na Japan.
Ya ce ayyukan farfado da ra’ayin nuna karfin soja, da kuma yawaita mu’amala da rukunonin sojoji da Japan ke yi, sun karya tanadin kundin tsarin mulkin Japan, da ma dokokin kasa da kasa, kana suna kalubalantar tsarin kasa da kasa na bayan yaki, kuma sun saba wa kalaman da Japan din ta furta, na ayyana kanta a matsayin “kasa mai kiyaye zaman lafiya.”
Bugu da kari, game da kalaman da ministan tsaron Japan ya yi a kwanan nan, Lin ya ce jerin maganganu da ayyukan da Japan ta yi a baya-bayan nan, sun haifar da barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankinta, kuma dole ne al’ummar duniya su kasance masu taka tsantsan sosai game da hakan.
Game da ziyarar aiki da ministan wajen Sin Wang Yi ya gudanar a kasar Kanada a kwanan nan kuwa, Lin ya bayyana cewa, Sin a shirye take ta ci gaba da zakulo hanyoyin da za a bi, don inganta sabuwar dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Kanada, da kuma habaka ci gaban dangantakar kasashen biyu, mai karko, kwanciyar hankali da dorewa.
Bugu da kari, Lin ya kuma yi bayani game da nasarar da Sin ta samu, ta kammala shugabancin kwamitin tsaron MDD na watan Mayu, yana mai cewa, Sin za ta ci gaba da karfafa hadin gwiwa da dukkan bangarori, tare da ci gaba da sauke nauyin da ke wuyanta na wanzar da zaman lafiya da ci gaban duniya. (Safiyah Ma)















Discussion about this post