Ɗan takarar gwamna na APC a jihar Nasarawa, Sanata Ahmed Aliyu Wadada, ya amince da tikitin takarar da jam’iyyarsa ta ba shi, tare da alƙawarin gina wa kan nasarorin gwamnatin yanzu da kuma kafa gwamnati mai mayar da hankali kan buƙatun al’umma.
Da yake jawabi a Lafia, Wadada ya gode wa mambobin APC bisa amincewar da suka nuna masa, yana mai cewa fitowarsa a matsayin ɗan takara nasara ce ga dimokuraɗiyya, da haɗin kai da ci gaban jihar. Ya kuma yabawa Gwamna Abdullahi Sule saboda irin ci gaban da ya ce gwamnatinsa ta samar a fannoni kamar ababen more rayuwa, da noma, da ilimi, da lafiya da tsaro.
Wadada ya bayyana laƙabin gwamnatinsa mai taken HEARTS Agenda, wanda ya ƙunshi bunƙasa ɗan Adam, da inganta tattalin arziƙi, da riƙon amana, da ci gaban karkara, da bunƙasa fasaha da ƙarfafa tsaro. Ya ce manufar ita ce samar da ƙarin damammaki ga matasa, jawo masu zuba jari da kuma haɓaka tattalin arziƙin jihar.
Ɗan takarar na APC ya yi kira ga sauran masu neman takara da magoya bayansu da su haɗa kai domin tabbatar da nasarar jam’iyyar a zaben 2027.
Ya kuma jaddada goyon bayansa ga manufofin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa sauye-sauyen tattalin arziƙin gwamnatin tarayya za su taimaka wajen samar da ci gaba mai ɗorewa a ƙasa.















Discussion about this post