Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya bukaci kasar Amurka da ta yi watsi da aniyarta, ta daukar matakin soji kan kasar Iran. Jami’in ya yi kiran ne a jiya Alhamis, yayin zaman kwamitin tsaron MDD dangane da halin da kasar Iran ke ciki.
Sun Lei, ya kara da cewa, a kwanan nan, Amurka ta rika fitar da jerin sanarwa dangane da halin da ake ciki a Iran, inda a fili ta rika yiwa Iran din barazanar amfani da karfin soji, wanda hakan ya kara tsananta yanayin dar-dar a yankin Gabas ta Tsakiya.
A bangarenta, har kullum kasar Sin na kira da a rungumi dalilan kulla kundin tsarin mulkin MDD da dokokin kasa da kasa. Sin ta shaida cewa, Iran kasa ce mai cin gashin kanta, kuma al’ummun kasar ne kadai ke da ikon yanke hukunci kan dukkanin harkokin da suka shafi kasarsu.
Bugu da kari, Sun Lei ya ce Sin ta lura da matukar damuwar akasarin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya dangane da batun fito-na-fito na soji. Tana kuma fatan Amurka da sauran sassa masu ruwa da tsaki, za su saurari kiraye-kirayen kasashen duniya da kasashen shiyyar, su kuma aiwatar da matakan wanzar da zaman lafiya da daidaito a yankin, maimakon aikata akasin hakan. Kana dukkanin kasashe su taka rawar gani wajen yaukaka zaman lafiya da shawarwari, da kaucewa duk wasu matakai da ka iya ruruta fito-na-fito ko kara iza wutar fitina. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post