A ranar 29 ga watan nan, Sun Lei, mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya, ya yi wani bayani cikin wata sanarwa bayan da kwamitin sulhun MDD ya kada kuri’a kan daftarin kudurin da ya shafi halin da ake ciki a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango (DRC). Ya yi kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa su bi ka’idojin takunkumin hana samar da makamai da kwamitin sulhun ya kakaba wa kungiyoyi masu dauke da makamai wadanda ba jami’an tsaron gwamnati ba a kasar ta DRC.
Ya ce Sin ta yi maraba da amincewa da kudirin daga daukacin mambobin kwamitin sulhun, wanda ya tsawaita takunkumin hana samar da makamai da sauran takunkumai kan kungiyoyi masu dauke da makamai a DRC, inda Sin ta kada kuri’ar amincewa da daftarin kudirin. Rikicin da ke faruwa a yankin gabashin DRC ya-ki-ci-ya-ki-cinyewa, wanda ya haifar da mutuwar fararen hula da dama da kuma korarsu daga gidajensu.
An samu karin shigar da makamai cikin kasar ba bisa ka’ida ba, wanda hakan ke kara ta’azzara rikici da kuma barazana ga tsaron yankin da kuma zaman lafiyar yankin, kuma Sin ta nuna matukar damuwa kan hakan. Kasar Sin tana kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa da su bi ka’idojin takunkumin hana samar da makamai na kwamitin sulhun MDD, da hana makaman fadawa hannun kungiyoyi masu dauke da makamai, sannan a ci gaba da karfafa aiwatar da kuduri mai lamba 2773 na kwamitin, tare da yin aiki cikin hadin gwiwa wajen cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma kawo karshen tashin hankali a yankin gabashin kasar ta DRC. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














