A yau Talata 30 ga watan nan na Yuni ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, da takwaransa na Seychelles Patrick Herminie, suka aikewa juna sakon taya murnar bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu.
Cikin sakonsa, shugaba Xi ya ce yana dora matukar muhimmanci ga bunkasar alakar kasarsa da Seychelles, ya kuma sha alwashin kara azama tare da shugaba Heminiyer, wajen mayar da wannan gaba ta bikin cikar alakar kasashensu shekaru 50 da kafuwa wani sabon mafari, na ci gaba da karfafa kawancen gargajiya, da gina shawarar ziri daya da hanya daya mai matukar inganci tare, kana da amfani da dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka wajen zurfafa cimma gajiyar bai daya, karkashin kudurorin hadin gwiwa na dandalin, da ingaza ci gaban bai daya, da jagorantar daga kawance bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Seychelles zuwa sabon matsayin, ta yadda hakan zai amfani al’ummun kasashen biyu.
A nasa sakon kuwa, shugaba Herminie cewa ya yi Sin ta jima da kasancewa muhimmiyar kawa mai kima ga kasar Seychelles, inda take samarwa kasar muhimmin goyon baya dake kyautata rayuwar al’umma, da walwala da cimma nasarar kudurorin bunkasa kasar ta Seychelles.
Kazalika, bangaren Seychelles na nacewa kan manufar kasar Sin daya tak a duniya, zai kuma ci gaba da karfafa hadin gwiwa tare da Sin karkashin shawarar ziri daya da hanya daya, da hada karfi wajen gina shawarar, da dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, da kuma ci gaba da zurfafa alakar kasashen biyu. Ban da haka, bisa gayyatar shugaban kasar Seychelles, Patrick Herminie, wakilin musamman na shugaban kasar Sin, Xi Jinping, kuma ministan sufuri, Liu Wei, ya halarci bikin ranar kasa domin murnar cika shekaru 50 da samun ‘yancin kan kasar Seychelles a Victoria, babban birnin kasar, ranar Lahadin da ta gabata.
Herminie ya gana da Liu a Victoria, jiya Litinin, inda lokacin ganawar tasu, Liu ya isar da gaisuwar shugaba Xi da kuma fatan alheri ga Herminie.
Liu ya ce, kasar Sin tana dora fifiko sosai kan yaukaka zumuncinta da Seychelles, kuma a shirye take, kamar ko da yaushe, ta goyi bayan Seychelles wajen gano hanyar zamanantarwa da ta dace da yanayin kasarta, da ci gaba da fadada hadin gwiwa mai amfanarwa ga juna a sassa daban-daban, da yin tsayin daka wajen goyon bayan juna kan batutuwan da suka shafi muhimman muradu da manyan abubuwa masu cin tuwo a kwarya, da kuma ciyar da dangantakar kasashen biyu gaba zuwa wani sabon mataki.
A nasa bangaren, Herminie ya yi matukar yabawa da zumuncin da ke tsakanin Seychelles da Sin, sannan ya jaddada cewa Seychelles na girmama dadaddiyar abotar da ke tsakanin kasashen biyu, tana kuma bin ka’idar Sin daya tilo a duniya sau-da-kafa, kana tana son zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin a fannoni daban-daban domin karfafa ci gaba da bunkasa alakar kasashen biyu. (Saminu Alhassan / Abdulrazaq Yahuza Jere)














