ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Da Takwaransa Na Seychelles Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Bikin Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 days ago
Xi

A yau Talata 30 ga watan nan na Yuni ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, da takwaransa na Seychelles Patrick Herminie, suka aikewa juna sakon taya murnar bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu.

Cikin sakonsa, shugaba Xi ya ce yana dora matukar muhimmanci ga bunkasar alakar kasarsa da Seychelles, ya kuma sha alwashin kara azama tare da shugaba Heminiyer, wajen mayar da wannan gaba ta bikin cikar alakar kasashensu shekaru 50 da kafuwa wani sabon mafari, na ci gaba da karfafa kawancen gargajiya, da gina shawarar ziri daya da hanya daya mai matukar inganci tare, kana da amfani da dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka wajen zurfafa cimma gajiyar bai daya, karkashin kudurorin hadin gwiwa na dandalin, da ingaza ci gaban bai daya, da jagorantar daga kawance bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Seychelles zuwa sabon matsayin, ta yadda hakan zai amfani al’ummun kasashen biyu.

A nasa sakon kuwa, shugaba Herminie cewa ya yi Sin ta jima da kasancewa muhimmiyar kawa mai kima ga kasar Seychelles, inda take samarwa kasar muhimmin goyon baya dake kyautata rayuwar al’umma, da walwala da cimma nasarar kudurorin bunkasa kasar ta Seychelles.

ADVERTISEMENT

Kazalika, bangaren Seychelles na nacewa kan manufar kasar Sin daya tak a duniya, zai kuma ci gaba da karfafa hadin gwiwa tare da Sin karkashin shawarar ziri daya da hanya daya, da hada karfi wajen gina shawarar, da dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, da kuma ci gaba da zurfafa alakar kasashen biyu. Ban da haka, bisa gayyatar shugaban kasar Seychelles, Patrick Herminie, wakilin musamman na shugaban kasar Sin, Xi Jinping, kuma ministan sufuri, Liu Wei, ya halarci bikin ranar kasa domin murnar cika shekaru 50 da samun ‘yancin kan kasar Seychelles a Victoria, babban birnin kasar, ranar Lahadin da ta gabata.

Herminie ya gana da Liu a Victoria, jiya Litinin, inda lokacin ganawar tasu, Liu ya isar da gaisuwar shugaba Xi da kuma fatan alheri ga Herminie.

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Liu ya ce, kasar Sin tana dora fifiko sosai kan yaukaka zumuncinta da Seychelles, kuma a shirye take, kamar ko da yaushe, ta goyi bayan Seychelles wajen gano hanyar zamanantarwa da ta dace da yanayin kasarta, da ci gaba da fadada hadin gwiwa mai amfanarwa ga juna a sassa daban-daban, da yin tsayin daka wajen goyon bayan juna kan batutuwan da suka shafi muhimman muradu da manyan abubuwa masu cin tuwo a kwarya, da kuma ciyar da dangantakar kasashen biyu gaba zuwa wani sabon mataki.

A nasa bangaren, Herminie ya yi matukar yabawa da zumuncin da ke tsakanin Seychelles da Sin, sannan ya jaddada cewa Seychelles na girmama dadaddiyar abotar da ke tsakanin kasashen biyu, tana kuma bin ka’idar Sin daya tilo a duniya sau-da-kafa, kana tana son zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin a fannoni daban-daban domin karfafa ci gaba da bunkasa alakar kasashen biyu. (Saminu Alhassan / Abdulrazaq Yahuza Jere)

Xi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
Xi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

MASU ALAKA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
Daga Birnin Sin

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Next Post
An Gudanar Da Kusan Ayyuka 500 Iri-iri Masu Ban Sha’awa A “Shekarar Cudanyar Jama’a Da Musanyar Al’adu Tsakanin Sin Da Afirka”

An Gudanar Da Kusan Ayyuka 500 Iri-iri Masu Ban Sha’awa A “Shekarar Cudanyar Jama’a Da Musanyar Al’adu Tsakanin Sin Da Afirka”

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.