ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Da Takwaransa Na Seychelles Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Bikin Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Xi

A yau Talata 30 ga watan nan na Yuni ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, da takwaransa na Seychelles Patrick Herminie, suka aikewa juna sakon taya murnar bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu.

Cikin sakonsa, shugaba Xi ya ce yana dora matukar muhimmanci ga bunkasar alakar kasarsa da Seychelles, ya kuma sha alwashin kara azama tare da shugaba Heminiyer, wajen mayar da wannan gaba ta bikin cikar alakar kasashensu shekaru 50 da kafuwa wani sabon mafari, na ci gaba da karfafa kawancen gargajiya, da gina shawarar ziri daya da hanya daya mai matukar inganci tare, kana da amfani da dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka wajen zurfafa cimma gajiyar bai daya, karkashin kudurorin hadin gwiwa na dandalin, da ingaza ci gaban bai daya, da jagorantar daga kawance bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Seychelles zuwa sabon matsayin, ta yadda hakan zai amfani al’ummun kasashen biyu.

A nasa sakon kuwa, shugaba Herminie cewa ya yi Sin ta jima da kasancewa muhimmiyar kawa mai kima ga kasar Seychelles, inda take samarwa kasar muhimmin goyon baya dake kyautata rayuwar al’umma, da walwala da cimma nasarar kudurorin bunkasa kasar ta Seychelles.

ADVERTISEMENT

Kazalika, bangaren Seychelles na nacewa kan manufar kasar Sin daya tak a duniya, zai kuma ci gaba da karfafa hadin gwiwa tare da Sin karkashin shawarar ziri daya da hanya daya, da hada karfi wajen gina shawarar, da dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, da kuma ci gaba da zurfafa alakar kasashen biyu. Ban da haka, bisa gayyatar shugaban kasar Seychelles, Patrick Herminie, wakilin musamman na shugaban kasar Sin, Xi Jinping, kuma ministan sufuri, Liu Wei, ya halarci bikin ranar kasa domin murnar cika shekaru 50 da samun ‘yancin kan kasar Seychelles a Victoria, babban birnin kasar, ranar Lahadin da ta gabata.

Herminie ya gana da Liu a Victoria, jiya Litinin, inda lokacin ganawar tasu, Liu ya isar da gaisuwar shugaba Xi da kuma fatan alheri ga Herminie.

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Liu ya ce, kasar Sin tana dora fifiko sosai kan yaukaka zumuncinta da Seychelles, kuma a shirye take, kamar ko da yaushe, ta goyi bayan Seychelles wajen gano hanyar zamanantarwa da ta dace da yanayin kasarta, da ci gaba da fadada hadin gwiwa mai amfanarwa ga juna a sassa daban-daban, da yin tsayin daka wajen goyon bayan juna kan batutuwan da suka shafi muhimman muradu da manyan abubuwa masu cin tuwo a kwarya, da kuma ciyar da dangantakar kasashen biyu gaba zuwa wani sabon mataki.

A nasa bangaren, Herminie ya yi matukar yabawa da zumuncin da ke tsakanin Seychelles da Sin, sannan ya jaddada cewa Seychelles na girmama dadaddiyar abotar da ke tsakanin kasashen biyu, tana kuma bin ka’idar Sin daya tilo a duniya sau-da-kafa, kana tana son zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin a fannoni daban-daban domin karfafa ci gaba da bunkasa alakar kasashen biyu. (Saminu Alhassan / Abdulrazaq Yahuza Jere)

Xi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
Xi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
Daga Birnin Sin

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
Daga Birnin Sin

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
Daga Birnin Sin

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
Next Post
An Gudanar Da Kusan Ayyuka 500 Iri-iri Masu Ban Sha’awa A “Shekarar Cudanyar Jama’a Da Musanyar Al’adu Tsakanin Sin Da Afirka”

An Gudanar Da Kusan Ayyuka 500 Iri-iri Masu Ban Sha’awa A “Shekarar Cudanyar Jama’a Da Musanyar Al’adu Tsakanin Sin Da Afirka”

LABARAI MASU NASABA

Xi

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Xi

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Xi

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Xi

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.