Kasar Sin ta karbi ragamar shugabancin kwamitin sulhu na MDD na wa’adin watan Mayu a jiya Jumma’a.
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD, kana shugaban kwamitin sulhu na wannan wata, Fu Cong, ya ce aikin kwamitin zai mayar da hankali sosai kan farfado da karfin ikon kundin tsarin mulkin MDD, da rawar da MDD ke takawa, da sa kaimi ga warware matsalar yankin gabas ta tsakiya ta hanyar siyasa, da kuma karfafa samar da zaman lafiya da ci gaba a kasashen Afirka.
Ya yi kira ga kasashen duniya da su dauki matakin gaggawa don karfafa ikon kundin tsarin mulkin MDD da kuma rawar da MDD ke takawa, a kokarin da ake yi na hana duniya “sake fadawa cikin tsarin rayuwar namun daji” da kuma “ceto zuriyoyin da za su biyo baya daga bala’in yaki.”
Dangane da kwanciyar hankali da ci gaban kasashen Afirka kuwa, jakadan na Sin ya ce, kwamitin sulhun zai ci gaba da mai da hankali kan nahiyar Afirka tare da tallafa wa kokarin warware matsalolin Afirka ta hanyar amfani da salo irin na Afirka. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post