ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Ceto Mata Da Yara 6 Daga Hannun ‘Yan Boko Haram A Jihar Borno

by Muhammad
2 months ago

Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabas, Operation HADIN KAI (OPHK), sun sake samun wata babbar nasara bayan ceto fararen hula shida da aka sace, tare da haɗa su da iyalansu a ƙauyen Ngoshe, ƙaramar hukumar Gwoza a Jihar Borno.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Lt. Col. Sani Uba, ya fitar ga manema labarai a Maiduguri ranar Asabar, ya ce wannan nasara ta biyo bayan ci gaba da kai hare-haren soji, ciki har da farmakin jiragen sama da aka kai kan maɓoyar ‘yan ta’adda a tsaunukan Mandara.

Ya bayyana cewa bisa sahihan bayanan sirri, sojojin OPHK yayin dawowa daga wani samame da suka kai cikin dare a safiyar Juma’a, 1 ga Mayu, 2026, sun tare tare da ceto mata da yara shida a yankin Amuda—wani wuri da babu kowa tsakanin Ngoshe da Gava a ƙaramar hukumar Gwoza, wanda aka san da zama hanyar zirga-zirgar ‘yan ta’adda.

ADVERTISEMENT

An bayyana sunayen waɗanda aka ceto da suka hada da Zainab Idris (Mai shekaru 18), Fatima Abubakar (Mai shekaru 17), Maimuna Abdulrashid (Mai shekaru 24), Muhammad Idris (Mai shekara 1), Sadiq Abdullahi (Mai shekara 7), da Fatima Abdulrashid (Mai shekara 5).

Binciken farko ya nuna cewa su na daga cikin mutanen da aka sace a harin da ‘yan ta’adda suka kai Ngoshe a ranar 3 ga Maris, 2026, inda aka tsare su a wani sansanin ‘yan ta’adda a Gava kafin su samu damar tserewa.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

A lokacin aikin ceton, sojojin sun fuskanci harbin daga ‘yan ta’adda da ke ƙoƙarin bin waɗanda suka tsere. Sai dai sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa, inda suka fafata na ɗan lokaci, lamarin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan ja da baya zuwa cikin tsaunuka.

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan nasara na da alaƙa da matsin lamba da ake ci gaba da yi wa ‘yan ta’adda, wanda ya raunana haɗin kansu tare da jefa su cikin ruɗani. Rahotannin sirri sun nuna cewa ‘yan ta’addan na cikin matsananciyar damuwa da firgici sakamakon asarar da suke yi da kuma tserewar waɗanda suka sace, ciki har da wata yarinya mai shekara 16 da aka tilasta mata aure da wani kwamandansu.

Bayan ceton, an ba waɗanda aka ceto agajin gaggawa tare da duba lafiyarsu a wani asibitin soji, kafin a miƙa su ga shugabannin al’umma.

Da misalin ƙarfe 2:00 na rana a ranar, an haɗa su da iyalansu ta hannun Wali na Ngoshe, Alhaji Shuaibu Dabawa, a wani yanayi mai cike da motsin zuciya wanda al’umma suka halarta.

Rundunar Sojojin Nijeriya ta tabbatar da ƙudirin ta na ci gaba da kare al’umma, ceto waɗanda aka sace, da kuma kawar da ‘yan ta’adda a dukkan yankunan Arewa maso Gabas.

Ta kuma ce ƙwarin gwiwar sojoji da ƙwarewarsu na nan daram, yayin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan da ƙarfi. An kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimaka wa ayyukan tsaro, don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban yankin.

Babban hafsan rundunar soji ya yaba wa sojojin bisa jajircewarsu, tare da ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da kai hare-hare domin mamaye fagen daga.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Tawagar Likitocin Sin A Nijar Ta Bayar Da Horo Na Farko Kan Agajin Gaggawa Da Ya Kai Ingancin Na Kasa Da Kasa

Tawagar Likitocin Sin A Nijar Ta Bayar Da Horo Na Farko Kan Agajin Gaggawa Da Ya Kai Ingancin Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.