Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabas, Operation HADIN KAI (OPHK), sun sake samun wata babbar nasara bayan ceto fararen hula shida da aka sace, tare da haɗa su da iyalansu a ƙauyen Ngoshe, ƙaramar hukumar Gwoza a Jihar Borno.
A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Lt. Col. Sani Uba, ya fitar ga manema labarai a Maiduguri ranar Asabar, ya ce wannan nasara ta biyo bayan ci gaba da kai hare-haren soji, ciki har da farmakin jiragen sama da aka kai kan maɓoyar ‘yan ta’adda a tsaunukan Mandara.
Ya bayyana cewa bisa sahihan bayanan sirri, sojojin OPHK yayin dawowa daga wani samame da suka kai cikin dare a safiyar Juma’a, 1 ga Mayu, 2026, sun tare tare da ceto mata da yara shida a yankin Amuda—wani wuri da babu kowa tsakanin Ngoshe da Gava a ƙaramar hukumar Gwoza, wanda aka san da zama hanyar zirga-zirgar ‘yan ta’adda.
An bayyana sunayen waɗanda aka ceto da suka hada da Zainab Idris (Mai shekaru 18), Fatima Abubakar (Mai shekaru 17), Maimuna Abdulrashid (Mai shekaru 24), Muhammad Idris (Mai shekara 1), Sadiq Abdullahi (Mai shekara 7), da Fatima Abdulrashid (Mai shekara 5).
Binciken farko ya nuna cewa su na daga cikin mutanen da aka sace a harin da ‘yan ta’adda suka kai Ngoshe a ranar 3 ga Maris, 2026, inda aka tsare su a wani sansanin ‘yan ta’adda a Gava kafin su samu damar tserewa.
A lokacin aikin ceton, sojojin sun fuskanci harbin daga ‘yan ta’adda da ke ƙoƙarin bin waɗanda suka tsere. Sai dai sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa, inda suka fafata na ɗan lokaci, lamarin da ya tilasta wa ‘yan ta’addan ja da baya zuwa cikin tsaunuka.
Sanarwar ta ƙara da cewa wannan nasara na da alaƙa da matsin lamba da ake ci gaba da yi wa ‘yan ta’adda, wanda ya raunana haɗin kansu tare da jefa su cikin ruɗani. Rahotannin sirri sun nuna cewa ‘yan ta’addan na cikin matsananciyar damuwa da firgici sakamakon asarar da suke yi da kuma tserewar waɗanda suka sace, ciki har da wata yarinya mai shekara 16 da aka tilasta mata aure da wani kwamandansu.
Bayan ceton, an ba waɗanda aka ceto agajin gaggawa tare da duba lafiyarsu a wani asibitin soji, kafin a miƙa su ga shugabannin al’umma.
Da misalin ƙarfe 2:00 na rana a ranar, an haɗa su da iyalansu ta hannun Wali na Ngoshe, Alhaji Shuaibu Dabawa, a wani yanayi mai cike da motsin zuciya wanda al’umma suka halarta.
Rundunar Sojojin Nijeriya ta tabbatar da ƙudirin ta na ci gaba da kare al’umma, ceto waɗanda aka sace, da kuma kawar da ‘yan ta’adda a dukkan yankunan Arewa maso Gabas.
Ta kuma ce ƙwarin gwiwar sojoji da ƙwarewarsu na nan daram, yayin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan da ƙarfi. An kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimaka wa ayyukan tsaro, don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban yankin.
Babban hafsan rundunar soji ya yaba wa sojojin bisa jajircewarsu, tare da ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da kai hare-hare domin mamaye fagen daga.















Discussion about this post