Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya ce kasar za ta ci gaba da aiki bisa tushen shawarwari hudu da shugaban kasar Xi Jinping ya gabatar, kana za ta hada kai da sauran al’ummun kasashen duniya, wajen samar da damar karfafa goyon bayan tattaunawar zaman lafiya, da taka rawar gani wajen cimma zaman lafiya mai dorewa a gabas ta tsakiya.
Kakakin ya bayyana hakan ne a Juma’ar nan, yayin da yake amsa tambayar da aka yi masa game da yanayin da ake ciki a Iran, inda ya ce tun bayan barkewar rikicin Iran, Sin ta yi aiki tukuru don ganin an kawo karshen tashin hankalin tare da dawo da zaman lafiya.
Ya kuma ce shugaba Xi ya gabatar da shawarwari hudu, dangane da karewa, da ingiza burin samar da zaman lafiya da daidaito a gabas ta tsakiya, kuma Sin da Pakistan sun gabatar da shawarwari biyar na maido da yanayin zaman lafiya da daidaito a yankin Gulf da gabas ta tsakiya.
Jami’in ya kara da cewa, matsayin Sin game da batun Iran a bayyana ne yake. Tashin hankalin da ya barke ya haifar da mummunar asara ga al’ummar Iran, da ma al’ummun sauran kasashen yankin.
Kazalika, tasirinsa na kara fadada, yayin da yakin ke kara takure ci gaban tattalin arzikin duniya, da tsarin rarraba hajojin masana’antu, da cinikayyar kasa da kasa, da daidaito a fannin hada-hadar makamashi ta duniya, wanda hakan zai illata moriya daukacin al’ummun kasa da kasa. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post