A daidai lokacin da harkokin siyasa ke kara kankama, inda ‘yan siyasa ke rububin neman matasan da za su yi amfani da su wajen taro da gangami a sassan kasar nan, inda ake amfani da wasu wajen ayyukan tarzoma na bangar siyasa, wani babban malamin addinin musulumci a Jihar Kano Sheikh Muhajjadina Sani Kano Alfalaki, wanda kuma shi ne shugaban masu ilimin Taurari na nahiyar Afrika, ya bukaci iyaye da gwamnati su sanya ido a kan iyalans su musamman matasa domin tabbatar ba a yiu amfani da su ba wajen tayar da tarzoma da sunan Bangar siyasa.
Sheikh Muhajjadina ya yi wannan tsokacin ne a tattaunawarsa da manema labarai a ofishinsa da ke Abuja a cikin wannan makon. Ya yi nuni da cewa, a kwai tashin hankali ba kadan ba yadda wasu ‘yan siyasa ke amfani da matassa bayan sun basu kayan maye a tarukan siyasa, “Za ka gansu dauke da makamai suna yi wa al’umma barazana, abin ke kai wa ga kisan kai ko munanan raunuka a wasu lokutta” in ji shi.
A kan haka sai malamin ya kalubalanci ‘yan siyasan da su dauko ‘ya’yansu su jagoranci wannan aikin inda gaske suna yi wa al’umma fatan alhairi. Ya kuma nemi gwamnati ba samar da dokar hana ayyukan bangar siyasa a kasar nan, “A tadani hukunci mai karfi ga duk wani dan siyasar da ya saba, maimakon sanya matasa a harkokin bangar siyasa ya kamata ‘yan siyasa su mayar da hankalinsu wajen samarwa matanmu sana’o’I da guraben karatu a matakai daban daban” in ji shi.
Ya kuma ja kunnen matasan a kan su guji fadawa tarkon miyagun ‘yan siyasa, domin kuwa ba suna yi musu fatan alhairi ba ne, “dole ku yi kanku karatun ta natsu” in ji shi.
Sheikh Muhajjdina dai ya shahara wajen ayyukan jinkan al’umma da talllafa wa mabukata a Jihar Kno da sassan Nijeriya..















Discussion about this post