Manufar soke harajin kwastam ta kasar Sin ga kasashen Afirka 53 masu huldar diflomasiyya da ita ta nuna irin jajircewar da Sin da Afirka ke yi wajen ba da gudummawa ga zaman lafiya da samun ci gaba cikin kwanciyar hankali a duniya, kamar yadda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana a yau Laraba, inda ya kara da cewa, Sin za ta ci gaba da inganta saukake cinikayya da Afirka.
Lin, ya yi wannan tsokaci ne a wani taron manema labarai na yau da kullun domin bayar da amsar wata tambaya game da manufar soke harajin kwastam ta Sin ga kasashen Afirka wadda za ta fara aiki daga ranar 1 ga Mayun 2026.
Lin ya kara da cewa, “Sin za ta ci gaba da tattaunawa da sanya hannu kan yarjejeniyoyin hadin gwiwa na tattalin arziki domin samun ci gaba na bai-daya tare da kasashen Afirka da suka kamata.
A lokaci guda kuma, za ta kyautata tsarin fitar da kayayyakin noma daga Afirka zuwa Sin tare da inganta saukake cinikayya tsakanin Sin da Afirka ba tare da tangarda ba.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post