Gwamnatin Jihar Filato, ta ce ta ƙwato kadarori sama da 60, ciki har da gine-gine, da kayayyakin aikin gini da motoci, a wani ƙoƙari da take ci gaba da yi na dawo da kadarorin gwamnati da ake zargin an karkatar da su tare da mamaye wa ba bisa ƙa’ida ba a faɗin jihar.
Shugaban Kwamitin Ƙwato Kadarorin Gwamnati, Janar Nash Yakubu mai ritaya, ne ya bayyana haka yayin da yake gabatar da rahoton wucin gadi ga Shugaban Hadiman Gwamnatin Jihar, Jerry Satmak, a birnin Jos.
Yayin gabatar da rahoton, shugaban kwamitin ya ce kwamitin, wanda ya shafe sama da shekara guda yana aiki, ya samu gagarumin nasara wajen ƙwato kadarorin gwamnati a faɗin jihar.
Yakubu, ya bayyana cewa kwamitin ya yi anfani da wata dabara na “Idan ka ga wani abu, to ka sanar” domin ƙarfafa wa al’umma gwiwa kan taimaka musu wajen gano kadarorin gwamnati da ake zargin an karkatar da su ko aka ɓoye.
Ya kuma jaddada aniyar gwamnati na dawo da dukkan kadarorinta da aka sama da faɗi da su tare da tabbatar da cewa an yi amfani da su yadda ya dace domin al’ummar jihar.















Discussion about this post