Mutane shida da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Jihar Katsina sun shaking iskar ‘yanci bayan dakarun rundunar 17 Birget ta sojojin Nijeriya sun ceto su yayin sintiri na yau da kullum a Ƙaramar Hukumar Faskari.
Mutanen da aka ceto sun haɗa da mata huɗu da yara maza biyu, inda dakarun da aka tura zuwa yankin Unguwan Doka suka same su a ranar Litinin, 29 ga Yuni, 2026, suna yawo a cikin daji bayan sun tsere daga hannun masu garkuwa da su.
A cikin wata sanarwa da Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na rundunar ta 17 Birget, Abayomi Adisa, ya fitar a ranar Talata, an bayyana sunayen waɗanda aka ceto da suka haɗa da Umaima Isiaku mai shekaru 30, Amina Isiaku mai shekaru 16, Safiya Isiaku mai shekaru 15, Ramatu Suleiman mai shekaru 30, Muhammad Shehu mai shekaru 4, da kuma Ibrahim Suleiman mai shekaru 2.
Rundunar sojin ta bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa ’yan bindigar sun yi garkuwa da mutanen ne daga yankin Unguwan Lado da ke Ƙaramar Hukumar Kankara a ranar 22 ga Yuni, 2026.














