Dakarun Rundunar Hadin Gwiwa ta Sojoji a Arewa maso Gabas karkashin ‘Operation HADIN KAI’ sun yi nasarar dakile wasu hare-hare da ake zargin mayakan ISWAP ne suka kai, inda suka kashe sama da ’yan ta’adda 20 a Jihar Yobe.
An kai hare-haren ne ga dakarun da ke jibge a Goniri, a daren Litinin, 9 ga Maris, har zuwa safiyar Talata, 10 ga Maris, 2026.
- Gwamna Uba Sani Bai Nuna Goyon Bayan Wani Ɗan Takarar Majalisa Ba – Gwamnatin Kaduna
- Lauyoyin Gwamnatin Kano Sun Tsunduma Yajin Aiki, Sun Rufe Ma’aikatar Shari’a
Sojojin sun bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Jami’in Yada Labarai na Rundunar Hadin Gwiwa, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a ranar Laraba.
A cewar sanarwar, ’yan ta’addan sun yi kokarin kai hare-hare daga bangarori da dama a lokaci guda domin kewaye sansanin dakarun.
“Dakarun Rundunar Hadin Gwiwa (Arewa maso Gabas) da aka jibge a Goniri karkashin Sekta 2 na ‘Operation HADIN KAI’ sun yi nasarar dakile hare-haren hadin gwiwa da ’yan ta’addan ISWAP suka kai kan sansaninsu da ke Goniri, Jihar Yobe, inda aka kashe sama da ’yan ta’adda 20,” in ji Uba.














