Dakarun Rundunar Hadin Gwiwa ta Sojoji a Arewa maso Gabas karkashin ‘Operation HADIN KAI’ sun yi nasarar dakile wasu hare-hare da ake zargin mayakan ISWAP ne suka kai, inda suka kashe sama da ’yan ta’adda 20 a Jihar Yobe.
An kai hare-haren ne ga dakarun da ke jibge a Goniri, a daren Litinin, 9 ga Maris, har zuwa safiyar Talata, 10 ga Maris, 2026.
- Gwamna Uba Sani Bai Nuna Goyon Bayan Wani Ɗan Takarar Majalisa Ba – Gwamnatin Kaduna
- Lauyoyin Gwamnatin Kano Sun Tsunduma Yajin Aiki, Sun Rufe Ma’aikatar Shari’a
Sojojin sun bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Jami’in Yada Labarai na Rundunar Hadin Gwiwa, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a ranar Laraba.
A cewar sanarwar, ’yan ta’addan sun yi kokarin kai hare-hare daga bangarori da dama a lokaci guda domin kewaye sansanin dakarun.
“Dakarun Rundunar Hadin Gwiwa (Arewa maso Gabas) da aka jibge a Goniri karkashin Sekta 2 na ‘Operation HADIN KAI’ sun yi nasarar dakile hare-haren hadin gwiwa da ’yan ta’addan ISWAP suka kai kan sansaninsu da ke Goniri, Jihar Yobe, inda aka kashe sama da ’yan ta’adda 20,” in ji Uba.















Discussion about this post