ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Bai Nuna Goyon Bayan Wani Ɗan Takarar Majalisa Ba – Gwamnatin Kaduna 

by Shehu Yahaya and Sulaiman
4 months ago
Uba sani

Gwamnatin Jihar Kaduna ta musanta wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta bisa zargin cewa gwamnan jihar, Uba Sani, ya goyi bayan wasu ’yan takara domin kujerun majalisar tarayya gabanin zabukan 2027 masu zuwa.

 

Gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin mara rushe tare da bukatar al’umma su yi watsi da shi baki daya.

ADVERTISEMENT
  • Lauyoyin Gwamnatin Kano Sun Tsunduma Yajin Aiki, Sun Rufe Ma’aikatar Shari’a
  • Kamfanonin Ketare Na Ganin Sabbin Fa’Idodin Ci Gaba Daga Sabbin Bukatun Kasuwar Sin

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Ahmed Maiyaki, ya sanya wa hannu , ya ce gwamna Uba Sani bai goyi bayan kowane dan takara ba, kuma bai fifita wani mai neman wata kujera ta zabe ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Sanarwar ta bayyana cewa gwamnan mai kishin dimokuradiyya ne, wanda ya yi imani da tsarin gaskiya da adalci, inda ’yan jam’iyya da masu ruwa da tsaki za su zabi ’yan takararsu ta hanyoyin da kundin tsarin jam’iyya ya tanada.

 

Sanarwa ta ci gaba da cewa ” Mun sanu wani sako mai rudani da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa gwamna ya goyi bayan wasu ’yan takara. Wannan ikirari karya ne gaba daya, kuma bai da tushe balle makama,”

 

Malam Maiyaki , ya kara da cewa a halin yanzu gwamnan ya fi maida hankali ne wajen inganta shugabanci nagari da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su kyautata rayuwar al’ummar jihar Kaduna, maimakon shiga batun goyon bayan ’yan takara tun kafin lokaci.

 

Sanarwar ta kuma gargadi mutane ko kungiyoyi da su guji yada labaran karya da bayanan siyasa marasa tushe, domin irin hakan na iya haifar da rudani a fagen siyasa tare da yaudarar jama’a.

 

Akan haka kwamishinan ya bukaci ’yan siyasa da magoya baya da sauran jama’a da su rika tabbatar da sahihancin labarai daga sahihan majiyoyi kafin yadawa, yana mai cewa sadarwa mai kyau na da muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

 

Maiyaki ya jaddada cewa gwamna Uba Sani zai ci gaba da mutunta hakkokin dimokuradiyya na dukkan masu neman takara, tare da tabbatar da cewa doka da ka’idoji ne za su jagoranci dukkan harkokin siyasa a jihar.

Uba sani
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
Uba sani
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi
  • Sulaiman
    Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC
  • Sulaiman
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP, Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.