Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun daƙile yunƙurin yin garkuwa da mutane tare da ceto mutane 14 da aka sace a Ƙaramar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.
Wata majiyar rundunar sojin ta ce an gudanar da aikin ne a ranar 25 ga watan Agusta, 2026, bayan sojoji sun samu sahihin bayani kan wasu mutane da ake zargin ‘yan bindiga ne a kusa da ƙauyen Magazu.
Sojojin sun gaggauta zuwa yankin inda suka tarar da wasu ‘yan bindiga na ƙoƙarin yin garkuwa da wasu mutane, ciki har da masu ababen hawa.
Sojojin sun buɗe musu wuta, lamarin da ya tilasta musu barin motarsu tare da tserewa zuwa cikin daji.
Daga bisani, sojojin sun gudanar da bincike a yankin tare da gano mutane 14 da aka yi garkuwa da su, inda suka ceto su.
Ɗaya daga cikin waɗanda aka ceto ya samu rauni, kuma nan take aka kai shi Babban Asibitin Tsafe domin kula da lafiyarsa.
Babu wani jami’in tsaro da ya ji rauni a yayin aikin.
Rundunar sojin ta ce nasarar aikin na nuna yadda dakarun Operation FANSAN YAMMA ke ci gaba da ƙoƙarin kare mutane tare da hana aikata laifuka a Jihar Zamfara.














