Rundunar ’Yansandan Jihar Nasarawa ta kama wani mutum da harsasai guda 174 na AK-47 a hanyar Toto zuwa Abaji.
An kama wanda ake zargin, mai suna Abubakar Abdullahi, ne a ranar Lahadi, 22 ga Yuni, 2026, lokacin da jami’an ’yansandan yankin Toto suke sintiri.
’Yansanda sun ce bayan sun bincike shi, sun gano harsasai 174 da ya ɓoye a jikinsa.
Kakakin rundunar ’yansandan jihar, SP Ramhan Nansel, ya ce wanda aka kama ya kasa bayyana daga ina ya samo harsasan, waye mai su, ko kuma inda yake kai su.
’Yansanda sun fara bincike domin gano ko akwai wasu mutane da ke da hannu a lamarin ko wata ƙungiyar masu aikata laifi da ka iya kasancewa tana da alaƙa da safarar harsasan.
Kwamishinan ’Yansandan Jihar Nasarawa, Shetima Jauro Mohammed, ya ce rundunar ta himmatu wajen yaƙi da aikata laifuka da kuma hana yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba a jihar.
Ya gargaɗi masu aikata laifuka cewa ba za a ba su mafaka a jihar ba, yana mai cewa ’yansanda za su ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri, sa ido da sauran matakan tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Rundunar ta kuma buƙaci jama’a da su riƙa bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka da tabbatar da zaman lafiya a jihar.














