Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike da ƙudurin kafa ‘yansandan jihohi zuwa Majalisar Dattawa domin kafa rundunar a faɗin jihohin Nijeriya.
An karanta ƙudirin a zauren Majalisar Dattawa a ranar Talata, inda Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, ya gabatar da wasiƙar shugaban ƙasar.
Ƙudirin na neman yin gyara ga Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na shekarar 1999 domin samar da tubalin doka da zai bai wa jihohi damar kafa da gudanar da rundunar ‘yansandansu.
A cewar Tinubu, ƙudirin na da nufin ƙarfafa tsarin tsaron N8jeriya tare da bai wa gwamnatocin jihohi damar taka rawa sosai wajen magance matsalolin tsaro.
Shugaban ƙasar ya ce ƙudirin ya ginu ne kan ƙoƙarin da Majalisar Dokoki ta fara, kuma ya ƙunshi matakan da za su tabbatar da cewa rundunar ‘yansanda ta tarayya da ta jihohi za su yi aiki tare yadda ya kamata.
Ya buƙaci Majalisar Dattawa da ta yi gaggawar nazari tare da amincewa da ƙudirin, yana mai bayyana shi a matsayin wani muhimmin ɓangare na gyaran tsarin tsaro da gwamnatinsa ke aiwatarwa.
Bayan karanta wasiƙar, Majalisar Dattawa ta miƙa ƙudirin ga Kwamitinta na Duba Kundin Tsarin Mulki domin ci gaba da aikin dokoki.
Wannan mataki na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun kiraye-kirayen kafa ‘yansandan jihohi domin taimakawa wajen magance matsalolin tsaro kamar ta’addanci, ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da sauran laifuka a faɗin Nijeriya.















Discussion about this post